• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki biyu da suka gabata, kafofin yada labaran Najeriya da dama sun buga bayanin da wani shahararren dan siyasa mai suna Dakuku Peterside ya rubuta, mai taken “Mene ne Najeriya za ta iya koya daga ci gaban kasar Sin a fannin samar da wutar lantarki?” Kasidar ta yi nuni da cewa, a shekarar 2000, ma’aunin samar da wutar lantarki na kasar Sin ya kai fiye da tiriliyan 1.3 KWH, kusan kashi daya bisa uku na lantarki da kasar Amurka ta samar. Sai dai ya zuwa shekarar 2024, karfin samar da wutar lantarki na kasar Sin ya zarce KWH tiriliyan 10, kusan ninki biyun na Amurka, kuma a daga cikin lantarkin, wanda aka samu daga makamashi mai tsabta ya kai kimanin kaso 55%. To, ko ta yaya kasar Sin ta cimma nasarar hakan? Dalilin da mista Peterside ya bayar ya shafi manufar musamman ta kasar Sin, ta tsara shirin raya kasa duk shekaru biyar-biyar, wanda ke da matsayi na wajibi tamkar doka. Ya ce, ci gaban da kasar Sin ta samu ya tabbatar da cewa, duk wata kasa za ta iya samun babban ci gaba ta hanyar tsayawa tsayin daka kan aiwatar da wasu nagartattun manufofi.

Tsokacin da Mista Peterside ya yi daidai ne. Saboda yin amfani da tsare-tsare na matsakaita, da na dogon lokaci wajen jagorantar aikin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma, hanya ce mai muhimmanci ga jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wajen gudanar da mulki a kasar. Tun daga shekarun 1950, kasar Sin ta fara tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen raya kasa na shekaru biyar biyar, kuma yanzu muna cikin wa’adin shirin raya kasa na shekaru 5 na 14, wanda kasar Sin ta tsara. Hakika “Shirin shekaru biyar” na farko zuwa na biyar sun baiwa kasar Sin damar kafa wani cikakken tsarin masana’antu da na tattalin arziki. Kana “Shirin shekaru biyar” na shida zuwa na tara, sun ba jama’ar kasar Sin damar samun kyakkyawan yanayin rayuwa gaba daya. Ban da haka, a cikin wa’adin ” shirin shekaru biyar” na goma zuwa na goma sha biyu, jimillar tattalin arzikin kasar Sin ya daga zuwa matsayi na biyu a duniya. Sa’an nan, a cikin shekaru kusan 10 da suka wuce, wato a cikin wa’adin “shirin shekaru 5” na 13 da na 14, kasar Sin ta gina al’umma mai ingancin rayuwa, kuma karfin tattalin arzikinta, da na kimiyya da fasaha, sun kai wani sabon matsayi. Bisa alkaluman da kasar Sin ta fitar, an ce, a yayin “shirin shekaru biyar” na 14 da za a kawo karshensa a bana, ana sa ran karuwar tattalin arzikin kasar Sin za ta zarce dalar Amurka triliyan 4.9, adadin da ya zarta jimillar tattalin arzikin kasar da ke matsayi na uku a duniya a fannin karfin tattalin arziki.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

Me ya sa “Shirin shekaru biyar” na kasar Sin ya iya haifar da irin wadannan dimbin alfanu? Dalili shi ne wasu halayen musamman na shirin. Bisa tsokacin da mista Li Zhongjie, masanin ilimin tarihin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya yi, “shirin shekaru biyar” na kasar Sin ya hada da halayen musamman na bin doka, da sanya moriyar jama’a a gaban komai, da daukar mataki bisa ainihin yanayin da ake ciki, da kokarin tabbatar da aiwatarwar manufofi.

A cikin wadannan halayen musamman, “sanya moriyar jama’a a gaban komai” na nufin: Na farko, yayin da ake tsara “Shirin shekaru 5”, dole ne a gudanar da bincike a tsanake a wurare daban-daban, da kuma sauraron ra’ayoyi daga kowane bangare. Misali, lokacin da aka tsara shirin “Shirin shekaru biyar” karo na 14, wasu shekaru biyar da suka gabata, baya ga gudanar da binciken, an kuma aiwatar da aikin neman ra’ayin jama’a kan layi, wato ta shafin yanar gizo na Intanet, a watan Agustan 2020, an kuma samu sama da shawarwari miliyan 1.018 daga masu amfani da yanar gizo. Na biyu, burin da ake neman cimmawa ta hanyar tsara “Shirin shekaru biyar” shi ne tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da kokarin biyan bukatun al’umma na fannoni daban daban. Saboda haka, duk wani “shirin shekaru 5” na kunshe da dimbin manufofin inganta rayuwar jama’a. Ma iya cewa, ana inganta zaman rayuwar jama’ar kasar Sin ne, ta hanyar aiwatar da “shirye-shiryen shekaru biyar” daya bayan daya.

Sa’an nan, “bin doka” yana nufin, yayin da aka tsara “shirin na shekaru biyar”, dole ne a bar dukkan jam’iyyun siyasa su yi tattaunawa mai zurfi a kansa, kana majalisar gudanarwar kasar Sin ta kula da aikin tsara shirin, kafin daga bisani majalissun dokokin kasar Sin su tantance shirin da kada kuri’a don zartar da shi, inda ake aiwatar da dukkan ayyukan bisa tsarin dimokuradiyya da kuma doka. Bugu da kari, kowace shekara, majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta kan yi bitar ci gaba da aka samu, a kokarin aiwatar da “shirin na shekaru biyar” da aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Ban da haka, bayan da aka tsara “shirin shekaru 5”, yana da muhimmanci a aiwatar da shi. A kasar Sin, bayan da aka gabatar da wani “shiri na shekaru 5”, dole ne a aiwatar da shi yadda ake bukata. Kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da majalisar gudanarwar kasar za su tsara salon aiwatar da dukkan ayyuka, da raba su ga sassa da yankuna daban-daban, don a aiwatar da su a matakai daban daban. Bayan haka, hukumomi daban daban su kan gudanar da ayyukan sa ido a tsakiyar wa’adin shirin, kuma za a tantance ainihin sakamakon da aka samu bayan karewar shirin.

Ta wadannan halayen musamman, za a iya ganin abubuwan da za su tabbatar da aiwatar da shirin na raya kasa: Na farko, kokarin kare muhimman muradun jama’a, da tabbatar da yanke shawara ta wata hanya mai dacewa, kuma bisa tsarin dimokuradiyya. Na biyu, yin amfani da tsare-tsaren shari’a wajen tabbatar da ingancin shirin da aka tsara, da mai da shi karkashin sa ido da aka yi masa. Na uku, tun daga gwamnatin tsakiya zuwa kananan hukumomi, dole ne a aiwatar da shirin raya kasa a tsanake, domin tabbatar da cimma burin da aka sanya a gaba. A cikin wadannan abubuwa, ana iya ganin ruhin dimokuradiyya da bin doka da oda, da kuma yanayin aiki na mai da hankali, da nuna sanin ya kamata, wadanda suka kasance tushen ci gaban kasar Sin.

A cewar mista Peterside, ta hanyar koyi da fasahohin kasar Sin, Najeriya za ta iya cin gajiyar dimbin albarkatun kasa da take da su, don tabbatar da cikar burinta na raya tattalin arziki. Ni ma na yi imanin cewa, Najeriya za ta iya yin hakan, tare da samun biyan bukata. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

Next Post

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

Related

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

2 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

6 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 weeks ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

2 weeks ago
Next Post
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.