• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

by Muhammad
12 hours ago
in Rahotonni, Siyasa, Tambarin Dimokuradiyya
0
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An haifi Muhammadu Buhari a ranar 17, ga Disamba, 1942, a garin Daura na Jihar Katsina, Nijeriya. Shi ne ɗa na 23 a cikin yaran Malam Harɗo Adamu, wani shugaba Fulani da ya fito daga garin Dumurkul da ke ƙaramar hukumar Mai’Adua ta jihar Katsina, da mahaifiyarsa Zulaihat. 

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari shi ne mutum na shida da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya a Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya rasu yana da shekaru 82 (2025 – 1942) a yammacin a ranar Lahadi a wani asibiti da ke birnin Landan bayan ya sha fama da doguwar rashin lafiya.

  • Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan
  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan

Ga wasu manyan abubuwa 10 da kowa zai so ya sani game da rayuwar Marigayi Buhari:

1. Hawa Shugabanci Karo Biyu – Soja Da Siyasa
Buhari ya shugabanci Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga 1983 zuwa 1985, sannan kuma aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a 2015 zuwa 2023.

2. Ƙwararren Soja, Ɗan Yaƙin Basasa
Ya shiga soja a 1962, ya samu horo a Burtaniya, kuma ya yi yaki a lokacin yaƙin basasa, inda ya jagoranci bataliya da manyan hare-hare a yankin gabas.

Labarai Masu Nasaba

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

3. Ƙaddamar Da Yaƙi Da Rashin Ɗa’a (WAI)
A mulkinsa na soja, Buhari ya ƙaddamar da shahararren shirin yaƙi da rashin ɗa’a, don ya gyara halayen jama’a da ƙarfafa kyawawan ɗabi’u da kishin ƙasa.

4. Mulki Tsauri A Shekarun 1980
Mulkinsa na soja ya ƙunshi dokoki masu tsauri da daure ’yan jarida da sallamar ma’aikata daj yanke hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi.

5. Shugabantar Kula Da Asusun PTF
A ƙarƙashin mulkin Janar Abacha, Buhari ya shugabanci PTF, inda aka yabawa ayyukansa na1 gaskiya da gina ababen more rayuwa.

6. Ya Yi Takara Huɗu, Ya Ci Zaɓe A Karo Na Ƙarshe
Buhari ya tsaya takara a 2003 da 2007 da 2011, amma sai a shekarar 2015 ya lashe zaɓe a matsayin shugaban ƙasa kuma ɗan jam’iyyar APC, inda ya kayar da Shugaba Goodluck Jonathan.

7. Ya Mayar Da Hankali Kan Yaƙi Da Rashawa Da Samar Da Tsaro
A mulkinsa na farar hula, ya mayar da hankali kan yaƙi da rashawa da yaƙi da Boko Haram da samar da shirye-shiryen tallafawa matasa kamar shirin N-Power.

8. Doguwar Jinya Ta Yi Tasiri A Mulkinsa
Ya sha barin ƙasa don neman lafiya, ciki har da watanni huɗu a 2017, lamarin da ya jawo damuwa da firgici kan yanayin lafiyarsa da tafiyar da mulki.

9. Ƙalubalen Zanga-Zangar #EndSARS
A 2020, gwamnatinsa ta fuskanci babbar zanga-zangar matasa kan cin zarafin ’yansanda (#EndSARS), wadda ta zama jigo a tarihin mulkinsa.

10. Miƙa Mulki Cikin Lumana Da Komawa Daura
A ranar 29 ga Mayu, 2023, ya miƙa mulki ga Shugaba Tinubu, sannan ya koma mahaifarsa garin Daura na jihar Katsina, bayan ya kammala aikin gwamnati na aƙaalla shekaru 50.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDauraKatsinaLandanLondonNigeriaNijeriyaRasuwaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Jennifer Simons Murnar Zama Shugabar Kasar Suriname

Next Post

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Related

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

2 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

2 days ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

2 days ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2 days ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

3 days ago
Next Post
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

July 13, 2025
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

July 13, 2025
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

July 13, 2025
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

July 13, 2025
Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

July 13, 2025
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

July 13, 2025
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

July 13, 2025
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

July 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.