• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

by Muhammad
4 months ago
Buhari

Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, ya bayyana alhini da kaɗuwa kan rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, yana mai bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan Nijeriya ‘yan kishin ƙasa da aka taɓa samu.

A cikin saƙon ta’aziyyarsa bayan sanarwar rasuwar tsohon shugaban ƙasar a Landan a sakamakon gajeriyar rashin lafiya, Abbas ya ce Buhari, wanda ya rasu yana da shekaru 82, ya sadaukar da yawancin rayuwarsa wajen hidimtawa ƙasar nan.

  • Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari
  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan

Kakakin ya bayyana Buhari a matsayin soja kuma dattijo wanda ya kafa suna da matsayin shugaba mai gaskiya da rikon amana, wanda rayuwarsa ta kasance cike da sauƙi da rashin kwaɗayin abin duniya da kyakkyawan ɗabi’u da suka sa aka yarda da shi sosai a fadin ƙasa.

Abbas ya ce Buhari yana daga cikin mutane biyu kacal da suka shugabanci Nijeriya a matsayin soja da kuma shugaban ƙasa a mulkin dimokuraɗiyya (bayan Olusegun Obasanjo), lamarin da ya ce wata dama ce ta musamman.

Abbas ya ambaci irin ƙaunar da talakawa musamman a Arewacin Nijeriya ke yi wa Buhari a matsayin ɗan siyasa, yana danganta hakan da dabi’unsa na gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Kazalika, Abbas ya bayyana yadda Buhari da wanda ya gada shi, Shugaba Bola Ahmed Tinubu da wasu suka kafa jam’iyyar APC, har lamarin ya yi ƙarfin da ya karɓe mulki daga PDP a 2015, bayan shekaru 16 suna mulki.

Abbas ya ce akwai jimami cikin rasuwar Buhari, bayan shekaru takwas a kan mulki, yanzu ya koma ga Allah domin hutu na har abada.

Kakakin ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Buhari da Sarkin Daura da al’ummar Daura da gwamnatin Jihar Katsina, har ma da Jihar Kaduna inda Buhari ya kwashe mafi yawan rayuwarsa yana zaune.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.