• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP

jam’iyyar NNPP ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Rufa’i Alkali, a ranar Larabar, ya bayyana cewa jam’iyyar a shirye take ta hada kai da wasu Jam’iyyun siyasa kafin zaben 2023 mai zuwa.

Mista Alkali, mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara ne kan harkokin siyasa, ya bayyana hakan a Legas a wani taron manema labarai.

  • Rikicin NNPP: Kwankwaso Ya Ci Amanarmu – Shekarau
  • Dalilin Da Yasa Ban Halarci Taron NBA Ba – Kwankwaso 

A cewarsa, jam’iyyar ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

“Jam’iyyun da ke son tattaunawa da jam’iyyar NNPP ba aibu ba ne su yi hakan a don samar da tafiya daya mai karfi, kuma dole ne mu bayyana ra’ayoyinmu kan makomar kasar nan.

“Dukkan jam’iyyu daidai suke a gaban doka.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

“Muna magana ne game da makomar Nijeriya,” in ji Mista Alkali, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa.

Ya kuma yi tir da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa a Nijeriya, yana mai cewa bai kamata mutane su zo a tattauna a fitar da dan takara daya tilo.

Tattaunawar kawance tsakanin jam’iyyun NNPP da Labour ta tsawon makonni ta gaza haifar da sakamako, shi ya sa ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun biyu – Mista Kwankwaso da Peter Obi – suka bayyana a matsayin ‘yan takara.

Alkali ya ce idan wata jam’iyya ta zauna don tattaunawa, dole ne su fara kokarin fahimtar kansu: mene ne suke da alaka da su – akida, hangen nesa, buri da kuma manufofin yin aiki tare.

Ya kara da cewa ya kamata jam’iyyu su amince da matakin kawance ko dai a majalisar wakilai, wakilai, dattijai, gwamna ko shugaban kasa.

“A siyasa muna magana ne game da kwazon aiki.”

Shugaban, ya ce Nijeriya ba za ta iya yin kuskure a 2023 ba, yana mai cewa jam’iyyar NNPP za ta bullo da sabbin dabarun gina tattalin arzikin kasa idan aka zabe shi.

Ya kara da cewa “NNPP tana wa Nijeriya shiri kuma za su kawo sauyi ga al’amuran siyasar kasar.”

Ya kara da cewa jam’iyyar NNPP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi girma a Nijeriya kuma nan ba da dadewa ba za ta samu goyon bayan mafi yawan ‘yan Nijeriya a fadin kasar.

Ya ce jam’iyyar NNPP za ta ci gaba da bin ka’idojinta na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

“Abin da Nijeriya ke bukata shi ne shugabancin da mutane za su amince da su kuma za su samar,” in ji Alkali, farfesa a fannin kimiyyar siyasa da tattalin arziki.

Akan tikitin takarar musulmi da musulmi, shugaban ya ce hakkin dan takara ne ya zabi abokin takararsa, yana mai cewa abin da ya kamata ya fi dacewa shi ne tunkarar kalubalen Nijeriya.

Ya kara da cewa: “Idan muna son kasar nan ta canza dole ne mu wuce batun maganar yankin yanki da tattaunawa kan addini.

“Mun wuce matakin sabani na yanki da ra’ayin addini.” (NAN)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023KwankwasoNNPPZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Ta’adda Ba Rauhanai Ba Ne, Dole Sojoji Su Yi Maganinsu – Buhari

Next Post

Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

12 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

15 hours ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

2 days ago
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Siyasa

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

3 days ago
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Siyasa

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

3 days ago
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
Siyasa

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

4 days ago
Next Post
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.