• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina kuma ɗaya daga cikin ‘yan takarar gwamnan jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa ya bayyana cewa duk wani yarfen siyasa da zarge-zarge da da cin mutunci da ake yi masa ana yi ne saboda yadda ya tsaya kai da fata wajan ganin ya tsare mutuncin gwamnatin Masari.

  • Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Dakta Mustapha Muhammad Inuwa ya furta haka ne a lokacin da yake yi wa dubun-dubatar magoya bayan sa da kungiyoyi da suka taro a ɗakin taro na Katsina motel a karon farko tun bayan faduwar zaɓen fidda gwani da ya yi jawabi.

“Amma shigarmu cikin gwamnati dukkan wata matsala da aka ji ko ta ɓata suna ko ta zarge zarge saboda alaƙarmu da gwamnati ce, ba wai dan mu ba, don haka mun tsare mutuncin gwamnati da shuwagabannin ta.”

Ya ci gaba da cewa mutane kuma suna ganin ana faɗin abubuwa iri-iri, da suke cikin gwamnati sun sani ba haka maganganu suke ba, mu ma mun sani ba haka suke ba, kuma abin bai taba samun mu ba, saboda mun san don Allah muke yi.” Inji shi

Haka kuma ya ƙara da cewa shi yanzu godiya yake yi wa Allah saboda ya bashi damar kuma cikin shekaru bakwai da aka yi aiki a wannan gwamnati “an riƙe amana, mun tsare mutuncin gwamnatin, mun tsare mutuncin shuwagabannin ta.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

Idan za a iya tunawa Mustapha Inuwa ya shafe shekara takwas yana adawa da Shema, a nan jihar Katsina ya jagoranci adawa ta shekara takwas, ya ce “muna da mutunci muna da ƙima shi ya sa lokacin da Zaɓen 2015 ya ƙara to duk wani wanda yake sha’awar cin zabe a jihar Katsina da suka danganta kan su da mu.”

“Kullum ina faɗi kuma ba zan daina faɗa ba, sai ranar da wani ya ƙaryata ni, zan daina faɗi, wanda zai ce ni da shi ko ma’aikacin gwamnati ko ɗan kwangil ko ɗan siyasa wanda muka yi hulɗar kuɗin gwamnati wanda na ce a yi wani abu da zan amfana da ya kai naira ɗaya ta hanyar da bai kamata ba, idan akwai na ce ya fito ya gaya wa duniya. An yi a can baya, lokacin da muke rigima da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema kuma na sake faɗi” Inji Inuwa

Haka zalika Mustapha Inuwa ya ce “idan mutum ya ce zai ci amana, wallahi tallahi ya baka tausai, saboda haka ba a cin amana a yi nasara, ba a yin sharri a yi nasara, to ni na riƙe amana, da yardar Allah duk damar da muka samu zamu ci gaba da riƙe amana.

“Haka kuma duk wanda yake ganin ɗabi’arsa ce ko al’adarsa ce cin amana to ya kuma da kanshi kuma ya tausaya zuri’arshi, saboda shi cin amana ba wai akanka kaɗai yake tsayawa ba, wallahi yana tafiya ga zuri’a ne.” In ji Mustapha


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Kaddamar Da Aikin Kafofin Watsa Labarai Na Kare Muhalli Na Sin Da Afirka

Next Post

An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

2 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

2 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

3 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

4 days ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

4 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

7 days ago
Next Post
An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.