• Leadership Hausa
Thursday, June 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara

by El-Zaharadeen Umar
12 months ago
in Siyasa
0
Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shahararren mawakin siyasar nan na ƙasar Hausa kuma mawakin shugaba Buhari, Dauda Abdullahi Kahutu Rarara, ya gargaɗi shugaban ƙasa Buhari da kar ya sake ya yaki, Bola Ahmad Tinubu, saboda ya taimaki shi a lokacin da yake buƙatar taimako.

Rarara ya bayyana haka cikin wani faifon bidiyo da ya karade kafafen yada labarai na zamani dangane da batun da wasu ‘ya ‘yan jam’iyyar APC ke cewa, Bola Ahmad Tinubu, ya yi wa shugaban ƙasa Buhari gorin taimako.

  • 2023: Tinubu Ne Mafi Dacewa Da Zama Shugaban Kasa —’Yan Kudu Maso Yamma
  • Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

Wannan magana da Bola ya yi da alama bata yi wa wasu daga cikin magoya bayan shugaba Buhari daɗi ba, saboda suna ganin babu wani dalili da zai sa, Bola Ahmad Tinubu, ya share wuri yana maganganu masu kama da suka ta kai -tsaye ga shugaba Buhari.

Inda har suke ganin kamar Bola Ahmad Tinubu yana ƙoƙarin wuce makaɗi da rawa, saboda neman mulki har yana ƙoƙarin cin fuskar shugaban ƙasa Muhammad Buhari.

Mawakin wanda ya ce Bola Ahmad Tinubu ya taimaki shugaban ƙasa, Muhammad Buhari, kuma ko shi Buhari ba zai ƙaryata hakan ba, ya ce har na kusa da Buharin ma sun san haka.

Labarai Masu Nasaba

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia

An ruwaito shugaban jam’iyyar APC na ƙasa Sanata Abdullahi Adamu yana cewa za su iya ɗaukar mataki akan Bola Tinubu dangane da wadancan kalamai na shi.

Shi kuwa mawakin na Buhari Dauda Kahutu Rarara ya ce wasu da ke ɗaukar wannan magana da zafi da yawan su ‘yan ‘good evening ne’ wato dai ‘yan ta more ne, amma ba su san da wancan zancen ba.

” An samu wani lokaci da Buhari ke buƙatar taimako kuma akwai ‘yan arewa da suke da halin da za su taimaka masa amma suka ƙi taimakonsa sai shi Bola Tinubu ɗin ne ya taimaki Buhari kuma ya samu abinda yake so” in ji shi.

Saboda haka a cewar Rarara babu wanda ya isa ya ce Bola Tinubu bai taimaki Buhari ba kuma shi Buharin ya sani, ya ce hatta mu ɗin nan mun sani.

Ya kara da cewa shi Bola Tinubu abokin siyasar Buhari ne, ya taimaki Buhari ya zama ɗan takara kuma yai zo ya taimaka aka kafa gwamnati da shi.

A cewar Rarara baban abinda zai yi na nunawa arewa dattako shi ne, ko dai ya goyi bayan Tinubu ko kuma ya bada dama ga kowa da kowa ya shiga zaɓen fidda gwani wanda Allah ya ba shikenan.

Tags: 2023APCBuhariRararaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adun Duanwu Na Kasar Sin Dake Da Tarihin Fiye Da Shekaru 2000

Next Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

Related

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima
Siyasa

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

5 days ago
Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia
Siyasa

Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia

2 weeks ago
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
Manyan Labarai

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

2 weeks ago
Tinubu Da Kwankwaso Sun Gana A Faransa
Manyan Labarai

Tinubu Da Kwankwaso Sun Gana A Faransa

2 weeks ago
Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba
Labarai

Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba

2 weeks ago
APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase
Siyasa

APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Ya Dace ‘Yan Siyasan Amurka Su Yi Tunani Kan Kalaman Elon Musk

Ya Dace ‘Yan Siyasan Amurka Su Yi Tunani Kan Kalaman Elon Musk

May 31, 2023
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Samar Da Yanayin Da Ya Dace Na Tattaunawa Tsakanin Rundunonin Sojin Kasashen 2

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Samar Da Yanayin Da Ya Dace Na Tattaunawa Tsakanin Rundunonin Sojin Kasashen 2

May 31, 2023
Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

May 31, 2023
Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

May 31, 2023
Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

May 31, 2023
Sin Na Goyon Bayan Gwamnatin Mali Wajen Yaki Da Ta’addanci Da Tabbatar Da Tsaron Kasa

Sin Na Goyon Bayan Gwamnatin Mali Wajen Yaki Da Ta’addanci Da Tabbatar Da Tsaron Kasa

May 31, 2023
An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

May 31, 2023
China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

May 31, 2023
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

May 31, 2023
Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

May 31, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.