ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
mustapha

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina kuma ɗaya daga cikin ‘yan takarar gwamnan jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa ya bayyana cewa duk wani yarfen siyasa da zarge-zarge da da cin mutunci da ake yi masa ana yi ne saboda yadda ya tsaya kai da fata wajan ganin ya tsare mutuncin gwamnatin Masari.

  • Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Dakta Mustapha Muhammad Inuwa ya furta haka ne a lokacin da yake yi wa dubun-dubatar magoya bayan sa da kungiyoyi da suka taro a ɗakin taro na Katsina motel a karon farko tun bayan faduwar zaɓen fidda gwani da ya yi jawabi.

“Amma shigarmu cikin gwamnati dukkan wata matsala da aka ji ko ta ɓata suna ko ta zarge zarge saboda alaƙarmu da gwamnati ce, ba wai dan mu ba, don haka mun tsare mutuncin gwamnati da shuwagabannin ta.”

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa mutane kuma suna ganin ana faɗin abubuwa iri-iri, da suke cikin gwamnati sun sani ba haka maganganu suke ba, mu ma mun sani ba haka suke ba, kuma abin bai taba samun mu ba, saboda mun san don Allah muke yi.” Inji shi

Haka kuma ya ƙara da cewa shi yanzu godiya yake yi wa Allah saboda ya bashi damar kuma cikin shekaru bakwai da aka yi aiki a wannan gwamnati “an riƙe amana, mun tsare mutuncin gwamnatin, mun tsare mutuncin shuwagabannin ta.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Idan za a iya tunawa Mustapha Inuwa ya shafe shekara takwas yana adawa da Shema, a nan jihar Katsina ya jagoranci adawa ta shekara takwas, ya ce “muna da mutunci muna da ƙima shi ya sa lokacin da Zaɓen 2015 ya ƙara to duk wani wanda yake sha’awar cin zabe a jihar Katsina da suka danganta kan su da mu.”

“Kullum ina faɗi kuma ba zan daina faɗa ba, sai ranar da wani ya ƙaryata ni, zan daina faɗi, wanda zai ce ni da shi ko ma’aikacin gwamnati ko ɗan kwangil ko ɗan siyasa wanda muka yi hulɗar kuɗin gwamnati wanda na ce a yi wani abu da zan amfana da ya kai naira ɗaya ta hanyar da bai kamata ba, idan akwai na ce ya fito ya gaya wa duniya. An yi a can baya, lokacin da muke rigima da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema kuma na sake faɗi” Inji Inuwa

Haka zalika Mustapha Inuwa ya ce “idan mutum ya ce zai ci amana, wallahi tallahi ya baka tausai, saboda haka ba a cin amana a yi nasara, ba a yin sharri a yi nasara, to ni na riƙe amana, da yardar Allah duk damar da muka samu zamu ci gaba da riƙe amana.

“Haka kuma duk wanda yake ganin ɗabi’arsa ce ko al’adarsa ce cin amana to ya kuma da kanshi kuma ya tausaya zuri’arshi, saboda shi cin amana ba wai akanka kaɗai yake tsayawa ba, wallahi yana tafiya ga zuri’a ne.” In ji Mustapha

mustapha
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.