ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
mustapha

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina kuma ɗaya daga cikin ‘yan takarar gwamnan jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa ya bayyana cewa duk wani yarfen siyasa da zarge-zarge da da cin mutunci da ake yi masa ana yi ne saboda yadda ya tsaya kai da fata wajan ganin ya tsare mutuncin gwamnatin Masari.

  • Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Dakta Mustapha Muhammad Inuwa ya furta haka ne a lokacin da yake yi wa dubun-dubatar magoya bayan sa da kungiyoyi da suka taro a ɗakin taro na Katsina motel a karon farko tun bayan faduwar zaɓen fidda gwani da ya yi jawabi.

“Amma shigarmu cikin gwamnati dukkan wata matsala da aka ji ko ta ɓata suna ko ta zarge zarge saboda alaƙarmu da gwamnati ce, ba wai dan mu ba, don haka mun tsare mutuncin gwamnati da shuwagabannin ta.”

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa mutane kuma suna ganin ana faɗin abubuwa iri-iri, da suke cikin gwamnati sun sani ba haka maganganu suke ba, mu ma mun sani ba haka suke ba, kuma abin bai taba samun mu ba, saboda mun san don Allah muke yi.” Inji shi

Haka kuma ya ƙara da cewa shi yanzu godiya yake yi wa Allah saboda ya bashi damar kuma cikin shekaru bakwai da aka yi aiki a wannan gwamnati “an riƙe amana, mun tsare mutuncin gwamnatin, mun tsare mutuncin shuwagabannin ta.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Idan za a iya tunawa Mustapha Inuwa ya shafe shekara takwas yana adawa da Shema, a nan jihar Katsina ya jagoranci adawa ta shekara takwas, ya ce “muna da mutunci muna da ƙima shi ya sa lokacin da Zaɓen 2015 ya ƙara to duk wani wanda yake sha’awar cin zabe a jihar Katsina da suka danganta kan su da mu.”

“Kullum ina faɗi kuma ba zan daina faɗa ba, sai ranar da wani ya ƙaryata ni, zan daina faɗi, wanda zai ce ni da shi ko ma’aikacin gwamnati ko ɗan kwangil ko ɗan siyasa wanda muka yi hulɗar kuɗin gwamnati wanda na ce a yi wani abu da zan amfana da ya kai naira ɗaya ta hanyar da bai kamata ba, idan akwai na ce ya fito ya gaya wa duniya. An yi a can baya, lokacin da muke rigima da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema kuma na sake faɗi” Inji Inuwa

Haka zalika Mustapha Inuwa ya ce “idan mutum ya ce zai ci amana, wallahi tallahi ya baka tausai, saboda haka ba a cin amana a yi nasara, ba a yin sharri a yi nasara, to ni na riƙe amana, da yardar Allah duk damar da muka samu zamu ci gaba da riƙe amana.

“Haka kuma duk wanda yake ganin ɗabi’arsa ce ko al’adarsa ce cin amana to ya kuma da kanshi kuma ya tausaya zuri’arshi, saboda shi cin amana ba wai akanka kaɗai yake tsayawa ba, wallahi yana tafiya ga zuri’a ne.” In ji Mustapha

mustapha
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.