ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
mustapha

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina kuma ɗaya daga cikin ‘yan takarar gwamnan jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa ya bayyana cewa duk wani yarfen siyasa da zarge-zarge da da cin mutunci da ake yi masa ana yi ne saboda yadda ya tsaya kai da fata wajan ganin ya tsare mutuncin gwamnatin Masari.

  • Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Dakta Mustapha Muhammad Inuwa ya furta haka ne a lokacin da yake yi wa dubun-dubatar magoya bayan sa da kungiyoyi da suka taro a ɗakin taro na Katsina motel a karon farko tun bayan faduwar zaɓen fidda gwani da ya yi jawabi.

“Amma shigarmu cikin gwamnati dukkan wata matsala da aka ji ko ta ɓata suna ko ta zarge zarge saboda alaƙarmu da gwamnati ce, ba wai dan mu ba, don haka mun tsare mutuncin gwamnati da shuwagabannin ta.”

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa mutane kuma suna ganin ana faɗin abubuwa iri-iri, da suke cikin gwamnati sun sani ba haka maganganu suke ba, mu ma mun sani ba haka suke ba, kuma abin bai taba samun mu ba, saboda mun san don Allah muke yi.” Inji shi

Haka kuma ya ƙara da cewa shi yanzu godiya yake yi wa Allah saboda ya bashi damar kuma cikin shekaru bakwai da aka yi aiki a wannan gwamnati “an riƙe amana, mun tsare mutuncin gwamnatin, mun tsare mutuncin shuwagabannin ta.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Idan za a iya tunawa Mustapha Inuwa ya shafe shekara takwas yana adawa da Shema, a nan jihar Katsina ya jagoranci adawa ta shekara takwas, ya ce “muna da mutunci muna da ƙima shi ya sa lokacin da Zaɓen 2015 ya ƙara to duk wani wanda yake sha’awar cin zabe a jihar Katsina da suka danganta kan su da mu.”

“Kullum ina faɗi kuma ba zan daina faɗa ba, sai ranar da wani ya ƙaryata ni, zan daina faɗi, wanda zai ce ni da shi ko ma’aikacin gwamnati ko ɗan kwangil ko ɗan siyasa wanda muka yi hulɗar kuɗin gwamnati wanda na ce a yi wani abu da zan amfana da ya kai naira ɗaya ta hanyar da bai kamata ba, idan akwai na ce ya fito ya gaya wa duniya. An yi a can baya, lokacin da muke rigima da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema kuma na sake faɗi” Inji Inuwa

Haka zalika Mustapha Inuwa ya ce “idan mutum ya ce zai ci amana, wallahi tallahi ya baka tausai, saboda haka ba a cin amana a yi nasara, ba a yin sharri a yi nasara, to ni na riƙe amana, da yardar Allah duk damar da muka samu zamu ci gaba da riƙe amana.

“Haka kuma duk wanda yake ganin ɗabi’arsa ce ko al’adarsa ce cin amana to ya kuma da kanshi kuma ya tausaya zuri’arshi, saboda shi cin amana ba wai akanka kaɗai yake tsayawa ba, wallahi yana tafiya ga zuri’a ne.” In ji Mustapha

mustapha
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

An Cimma Cikakkiyar Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-14

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.