• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

by Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 6 ga wata ne aka kaddamar da wani taro na tsawon kwanaki 15 tsakanin Sin da kasar Senegal, domin ba da horo kan cikakken tsarin masana’antar gyada, wanda ya tattaro mahalarta 14 daga kasar Senegal, wadanda suka hada da masu bincike, da jami’an gwamnati da kuma ‘yan kasuwa.

Aikin gona wani gagarumin bangare ne cikin tattalin arzikin kasar Senegal, inda noman gyada ya kasance muhimmiyar hanyar samar da kudin shiga da aikin yi, Sai dai kamar yadda muka sani, har yanzu kasashen Afrika ne koma baya a bangaren amfani da fasahohin zamani a ayyukan gona da masana’antu, wadanda ake matukar bukata domin samun ci gaba.

  • Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO
  • Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

Idan muka kwatanta su da Sin, za mu ga wagegen gibin dake akwai tsakanisu a wannan bangare. Kasar Sin ba ta da arzikin filin noma kamar kasashen Afrika, amma tana iya dogaro da abun da take samu wajen ciyar da al’ummarta, sabanin kasashen Afrika da har yanzu suke fama da matsalar yunwa saboda rashin wadatar abinci.

Mene ne dalilin bambancin dake tsakanin bangarorin biyu? Kasancewarta jajirtacciya, kasar Sin ta yi kokarin lalubo hanyoyin ciyar da kanta ta hanyar amfani da fasahohi da sabbin dabarun raya aikin gona. Irin wannan basira da gogewa ta kasar Sin, kasashen Afrika suke bukata muddun suna neman zama masu dogaro da kansu.

Karin maganar Sinawa dake cewa, ka koya wa mutum su maimakon ba shi kifi abu ne da muka gani a zahiri. Misali shi ne yadda a ko da yaushe wasu kan yi amfani da tallafin kudi da suke bayarwa wajen yin barazana da shiga harkokin gidan ’yantattun kasashe da yadda hakan ke haifar da koma baya da jefa kasashen da suka dogara da tallafi cikin mummunan yanayi.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

Na san zuwa yanzu kowa zai amince cewa, kasar Sin ta bullo da sabuwar dabara ta abota da hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa da ya bambanta da ta masu son cin zali da neman iko. Koyar da fasahohin da za su taimakawa kasashe masu tasowa musamman kasashen Afrika, zai kai su ga habaka ayyukansu da samar da sabbin dabarun ci gaba ta yadda za su habaka noma a cikin gida da sarrafa albarkatu har ma da shigar da su kasuwannin duniya. Wannan zai kai su ga samun wadata da ba su damar tsayawa da kafarsu. Tabbas wannan ya nuna cewa, kasar Sin aminiya ce ta kwarai mai son ganin dorewar ci gaban kasashe maimakon amfani domin mayar da su masu amshin shata, lamarin da zai kai ga cimma burin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

Next Post

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Related

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

3 hours ago
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar
Daga Birnin Sin

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

3 hours ago
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

4 hours ago
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

5 hours ago
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

5 hours ago
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

8 hours ago
Next Post
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.