ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

by Sulaiman
11 months ago
Karin magana

A ranar 6 ga wata ne aka kaddamar da wani taro na tsawon kwanaki 15 tsakanin Sin da kasar Senegal, domin ba da horo kan cikakken tsarin masana’antar gyada, wanda ya tattaro mahalarta 14 daga kasar Senegal, wadanda suka hada da masu bincike, da jami’an gwamnati da kuma ‘yan kasuwa.

Aikin gona wani gagarumin bangare ne cikin tattalin arzikin kasar Senegal, inda noman gyada ya kasance muhimmiyar hanyar samar da kudin shiga da aikin yi, Sai dai kamar yadda muka sani, har yanzu kasashen Afrika ne koma baya a bangaren amfani da fasahohin zamani a ayyukan gona da masana’antu, wadanda ake matukar bukata domin samun ci gaba.

  • Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO
  • Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

Idan muka kwatanta su da Sin, za mu ga wagegen gibin dake akwai tsakanisu a wannan bangare. Kasar Sin ba ta da arzikin filin noma kamar kasashen Afrika, amma tana iya dogaro da abun da take samu wajen ciyar da al’ummarta, sabanin kasashen Afrika da har yanzu suke fama da matsalar yunwa saboda rashin wadatar abinci.

ADVERTISEMENT

Mene ne dalilin bambancin dake tsakanin bangarorin biyu? Kasancewarta jajirtacciya, kasar Sin ta yi kokarin lalubo hanyoyin ciyar da kanta ta hanyar amfani da fasahohi da sabbin dabarun raya aikin gona. Irin wannan basira da gogewa ta kasar Sin, kasashen Afrika suke bukata muddun suna neman zama masu dogaro da kansu.

Karin maganar Sinawa dake cewa, ka koya wa mutum su maimakon ba shi kifi abu ne da muka gani a zahiri. Misali shi ne yadda a ko da yaushe wasu kan yi amfani da tallafin kudi da suke bayarwa wajen yin barazana da shiga harkokin gidan ’yantattun kasashe da yadda hakan ke haifar da koma baya da jefa kasashen da suka dogara da tallafi cikin mummunan yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Na san zuwa yanzu kowa zai amince cewa, kasar Sin ta bullo da sabuwar dabara ta abota da hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa da ya bambanta da ta masu son cin zali da neman iko. Koyar da fasahohin da za su taimakawa kasashe masu tasowa musamman kasashen Afrika, zai kai su ga habaka ayyukansu da samar da sabbin dabarun ci gaba ta yadda za su habaka noma a cikin gida da sarrafa albarkatu har ma da shigar da su kasuwannin duniya. Wannan zai kai su ga samun wadata da ba su damar tsayawa da kafarsu. Tabbas wannan ya nuna cewa, kasar Sin aminiya ce ta kwarai mai son ganin dorewar ci gaban kasashe maimakon amfani domin mayar da su masu amshin shata, lamarin da zai kai ga cimma burin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Fa’iza Mustapha)

Karin magana
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • Sulaiman
    Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

MASU ALAKA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
Next Post
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Karin magana

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.