• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Bankado Wadanda Suka Kashe Dattijuwa – Gwamnan Gombe Ga Jami’an Tsaro

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
A Bankado Wadanda Suka Kashe Dattijuwa – Gwamnan Gombe Ga Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi suka kan kisan gillar da aka yi wa Aishatu Abdullahi mai shekara 58, mai ‘ya’ya takwas a unguwar Jekadafari da ke cikin garin Gombe, inda ya bayyana lamarin a matsayin na rashin imani. 

Gwamnan ya umarci ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro da abin ya shafa da su kaddamar da bincike tare da tabbatar da an gurfanar da wadanda suka aikata wannan danyen aiki a gaban kuliya.

  • Abin Da Ya Sa Muka Sa Takin Zamani Cikin Tallafin Jama’a – Gwamnan Filato
  • Messi Zai Iya Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana

Ya sha alwashin cewa Jihar a karkashin jagorancinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihar, kamar yadda Ismaila Uba Misilli Babban Darakta Yada labarun gwamnan jihar ya nakalto ta cikin wata sanarwar.

“Ba za mu taba lamuntar aikata laifuka ba, kuma wannan lamarin zai kara karfafa aniyarmu na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jiharmu”.

“Ina bayyanawa cewa wadanda suka aikata wannar aika-aikar ba za su sha ba har sai sun fuskanci shari’a, mun umurci jami’an tsaro su bi diddigin waɗanda suka aikata wannan aika-aika domin su girbi sakamakon mugun aikin da suka aikata.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Ya mika jaje ta ta’aziyyar gwamnati da al’ummar Jihar Gombe ga iyalan marigayiyar.

“Bayanin wannan lamari kamar yadda ‘yan sanda suka bayar tun farko, wani abu ba ne mai ban tsoro da takaici. Zukatanmu sun kadu tare da tausayawa iyalan wacce ta rasa ranta, wadanda suke cikin jimami maras misaltuwa, da kuma al’ummar Jekadafari da ma dokacin al’ummar Jihar Gombe, waɗanda suke cikin takaici sakamakon wannan mummunan lamari.”

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar su kwantar da hankalinsu su kuma sanya ido don magance duk wata barazanar tsaro, yana mai alƙawarin cewa Jihar Gombe ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin da take da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Messi Zai Iya Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana

Next Post

Tsohon Dan Wasan Manchester United, Charlton Ya Mutu

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

55 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Tsohon Dan Wasan Manchester United, Charlton Ya Mutu

Tsohon Dan Wasan Manchester United, Charlton Ya Mutu

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.