• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dauki Matsayi Na Kasashe Masu Tasowa Don Samun Daidaitaccen Ra’ayi

by CGTN Hausa
2 years ago
Ra'ayi

A wajen taron cudanyar wayewar kai na Sin da Afirka karo na 3, da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan baya, darektan cibiyar nazarin harkokin ci gaban kasa ta kasar Uganda, kuma babban mai nazari, Allawi Ssemanda, ya yi jawabi, inda ya ambaci batun shafawa huldar dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin kashin kaza, da wasu kafofin watsa labaru na kasashen yamma suka dade suke yi. Ya ce, “A duk lokacin da kafofin yada labaru na kasashen yamma suka yi magana kan hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin, kusan ba su taba ambatar yadda ake hadin gwiwa don amfanin juna ba, maimakon haka su kan yada wasu karairayin cewa, Sin na dana ‘tarkon bashi’, ko kuma ‘kasar Sin za ta yi mulkin mallaka a kasarku’.”

Hakika, a shekarun baya, yayin da ake ta samun rikice-rikice a duniya, kasar Amurka da wasu kawayenta na yammacin duniya suna kara shafa wa hadin gwiwar Sin da Afirka da kashin kaza, kuma ta hanyoyi daban daban. Alal misali, cibiyar nazarin manufofin raya kasa na duniya ta jami’ar Boston ta kasar Amurka, ta gabatar da wani rahoton bincike a kwanan baya, inda ta yi suka kan jarin da kasar Sin ke zubawa kasashen Afirka, cewa wai “kasar Sin ba ta mai da hankali kan zuba jari ga bangaren makamashin da ake iya sabuntawa a kasashen Afirka ba”.

  • Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa
  • Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Sai dai wannan magana sam ba gaskiya ba ce. Idan mun dauki aikin raya makamashi mai tsabta a kasar Najeriya a matsayin misali, za mu ga yadda kamfanonin kasar Sin suka zuba jari gami da daukar nauyin gina madatsar ruwa ta Zungeru, wadda ta fi girma a kasar Najeriya. An ce wutar lantarkin da madatsar ruwan ke samarwa za ta iya biyan bukatun babban birni irinsa Abuja guda 2.

Hakika a shekarun baya, kasar Sin ta riga ta aiwatar da daruruwan ayyukan raya makamashi mai tsabta, da na bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, a nahiyar Afirka, ta yadda take kan gaba a duniya ta fuskar hadin kai da kasashen Afirka a wadannan fannoni. Misali, a kasar Morocco, tashar samar da wutar lantarki ta zafin hasken rana ta Noor, da wani kamfanin kasar Sin ya gina, tana samar da wutar lantarki mai tsabta ga magidanta fiye da miliyan 1, ta yadda aka canza yanayin da kasar Morocco ke ciki na dogaro kan wutar lantarki na kasashen waje. Kana a kasar Afirka ta Kudu, tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska ta De Aar, da wani kamfanin Sin ya zuba jari gami da gina ta, ta kan samar da wutar lantarki da yawanta ya kai KWH miliyan 760 duk shekara, don biyan bukatun magidanta dubu 300. Ban da haka, a kasar Uganda, ba a jima da kammala aikin kafa na’urar samar da wutar lantarki na karshe ba, a tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa ta Karuma, da wani kamfanin kasar Sin ya gina, matakin da ya sa karfin samar da wutar lantarki na kasar ya karu da kimanin kashi 50%.

To, sai dai me ya sa kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya ke son shafawa kasar Sin da huldar hadin gwiwa dake tsakaninta da kasashen Afirka da kashin kaza? A cewar Allawi Ssemanda, “ Kasashen yamma suna kallon kansu kamar masu gida ne, wadanda suka fi ilimi. Saboda haka suna son shawo kan sauran kasashe. Kana sun cika girman kai inda suke ganin cewa duk wani abu mai amfani, sai daga wajensu ne zai iya fitowa.”

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Sai dai yaya aikin “shawo kan” sauran kasashe da kasar Amurka da kawayenta suke? Allawi Ssemanda ya ce, “ Dukkan kasashen Afirka sun tuna yadda kasashen yamma suka tilasta musu, don su gudanar da shirin daidaita tsare-tsaren tattalin arizki, tare da zummar gurgunta su. ” Yana nufin gyare-gyaren da kasashen yamma suka tilastawa kasashen Afirka don su yi, ta bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, tun daga tsakiyar shekarun 1970, wadanda suka shafi matakan raba dukiyoyin gwamnati ga masu jari hujja, da samar da ’yanci ga ayyukan zuba jari da ciniki, da dai sauransu. Matakan da suka haddasa koma bayan tattalin arzikin kasashen Afirka, da faduwarsu cikin tarkon bashi na gaske.

Ban da haka, Mista Ssemanda ya ce, “Akidar ’yanci ta Liberalism ta kasashen yamma ba wata daidaitacciyar akidar siyasa ba ce, maimakon haka, ta kasance wani karfi ne dake neman yin habaka a kai a kai.” Wannan ra’ayinsa ya samu karin tabbatarwa daga wata masaniyar ilimi mai alaka da kasashen Afirka ta kasar Sin Liu Haifang. Wani kundin da ta rubuta ya nuna cewa, akidar ’yanci ta kasashen yamma ta sa kasashen Afirka shigar da dimbin jari daga kasashen waje ba tare da wata kayyadewa ba, abin da ya sa kasashen Afirka zama ’yan amshin shatar sauran bangarori. Inda masu jari suka hada baki da masu iko dake wurare daban daban, da wadanda ke wakiltar wasu kabilu, da addinai, don kafa dimbin gungun dake neman kare moriyar kansu. Hakan ya sa aka samu ikon tabbatar da manufofin kasa, da sanya dimbin kasashe dake nahiyar Afirka rasa karfin kare moriyar kasa.

Da wannan za mu san cewa, ra’ayin wani yana da alaka da matsayinsa. Idan an dauki matsayi na kasashen yamma, za a yi tsammanin cewa, duk wani matakin da kasashe masu tasowa suka dauka ba zai yi daidai ba, ban da hakuri da ci da gumi da bautarwa da kasashen yamma suka yi musu. Saboda haka dole ne kasashe masu tasowa su dauki matsayi na kansu, da kokarin kare moriyar kasa, da tantance abubuwa bisa yanayi na gaske da suke ciki, ta yadda za a iya samun daidaitaccen ra’ayi, tare da daukar matakai masu dacewa. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
Next Post
Fataucin Yara

Bukukuwan Sallah: Rundunar 'Yansanda Ta Kama Bata-gari 104 Da Ake Zargi Da Aikata Laifuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.