• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Koyi Darasi Daga Tarihi

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Tarihi

A ranar 9 ga wata bisa agogon wurin, an shirya gagarumin bikin cika shekaru 80 da cimma nasara a yakin kare kasa na tsohuwar Tarayyar Soviet a filin “Red Square” na birnin Moscow. Shugaban kasar Sin Xi Jinping da ma shugabanni daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa sama da 20 sun halarci bikin bisa gayyatar da aka yi musu.

Ga duniya, shekarar 2025 tana da ma’ana ta musamman. Shekara ce ta cika shekaru 80 da nasarar da jama’ar kasar Sin ta cimma na yakar maharan Japan, da ta babban yakin kare kasa na tsohuwar Tarayyar Soviet, da ta yakin kin harin ‘yan mulkin danniya na duniya, har ma da cika shekaru 80 da kafuwar Majalisar Dinkin Duniya.

  • INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Sinawa kan ce, “A Koyi darasi daga tarihi”. Darussan zafi na yakin duniya na biyu sun gargadi mutane cewa, son zuciya da wariya, kiyayya da yaki za su kawo masifa da wahala ne kawai, yayin da mutunta juna, zaman tare cikin daidaito, ci gaba cikin lumana, da samun wadata tare su ne hanya madaidaiciya a duniya. Amma abin takaici ne cewa, a yau, bayan shekaru 80 da suka gabata, wasu mutane sun manta da darussan, kuma suna bin ra’ayin kashin kai, danniya ko babakere da zalunci, kana da sun ta yayata kalaman na wai “rashin amfanin Majalisar Dinkin Duniya” da “rashin inganci na dokokin kasa da kasa”.

A wannan muhimmin lokaci, shugaba Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Rasha, inda ya halarci bikin cika shekaru 80 da cimma nasara a yakin kare kasa na tsohuwar Tarayyar Soviet, lamarin da ya sanar da duniya cewa, ba za a manta da tarihi ba, kuma zaman lafiya ba a samunsa cikin sauki. Don haka, dole ne Sin da Rasha su kiyaye adalci na kasa da kasa tare.

A yayin tattaunawar da suka yi a birnin Moscow a wannan karo, shugabannin kasashen biyu sun amince da yada ra’ayin gaskiya game da tarihin yakin duniya na biyu, da kiyaye fada-a-ji da matsayin Majalisar Dinkin Duniya, da kiyaye adalci a duniya. Wannan ya nuna alkibla ga al’ummomin duniya, ta kare nasarorin da aka samu a yakin duniya na biyu, da kuma tinkarar hadari da kalubale masu yawa. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.