• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad

by Amina Bello Hamza
2 years ago
in Tattaunawa
0
A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashiyar ‘yar kasuwa mai fatan ganin ta dogara da kanta Fatima Sa’ad, ta yi wa Leadrship Hausa bayanin rayuwarta da yadda ta tsunduma a harkar kasuwanci, ci gaban ta samu da ma kalubalen da fuskata a harkar, in a cikin hakan ta ba wa iyaye shawarar su tashi tsaye wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance da wakiliyarmu Amina Bello Hamza.

Da farko za mu so ki bayyana mana sunanki

Sunana Fatima Sa’ad Aliyu. An haife ni a Tudun Jukun da ke Zariya, na yi karatuna tun daga Nursery har na kammala sikandirena, yanzu haka ina karatu a Nuhu Bamalli polytechnic Zariya.

Ko Malamar Na Da Aure?

A a ba ni da aure

Labarai Masu Nasaba

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu

Wace sana’a kike yi a halin yanzu?

Ina sayar da duk wani nau’i na sutura, (Hajibai, Atamfa, shadda, Leshi, yadi na maza da mata, jakunkuna, takalma, da dai sauran su. Sanan ina sana’ar hannu Hada jakunkuna, takalma, zannuwan gado, da fululunka kujeru da kuma sa’ar Aya da Riidi).

Menene ya baki sha’awar fara wannan sana’a?

To ni dai ba zance ga wani abu da ya ba ni sha’awa ba saboda tun ina firamare na nake sana’a irin ta dalibai a makarata irin su iloka, Aya, lokacin ban san ma mai zan yi da kudin ba kawai ni dai ina jin dadi in ji ana cewa ki bani abu kaza.

To daga baya ne da girma ya fara zuwa sanan na ji sha’awar ka san cewa kamar mamana saboda ita ‘yar kasuwa ce ba ta iya zama ba sana’a gaskiya.

Idan mutum na son fara wannan sana’ar wani abu zai tana da don samun cikakkiyar nasara?

To da farko de dole ne ya fara sa rai shi sa’ana zai yi kuma ya dauke ta da mahimmaci, saboda idan bai dauke ta da mahimmanci ba ba zai iya juriya akan ta ba, sanan sai jari ko da bashi da yawa in dai bai raina ba to lallai wata rana zai ga amfanin haka, cikakkiyar nasara ba’a samun ta haka dole sai ka hadu da jarabawa da kuma kalubale, to a nan za ka yi hakuri da juriya sai Allah ya taimake ka har ka kai ga cin nasara a rayuwarka.

Ta Yaya Kike Tallata Hajojinki?

Ina tallata hajata ne ta kafar sada zumunta (social media). Sannan duk inda zan shiga makaranta ce gidan biki kai koma ina ne to zan tallata hajata, haka ma cikin kawayena.

Kuma Alhamdu lillahi muna ganin alfanun haka.

Ko kin taba samun tallafin gwamnati ko wata hukuma a harkar kasuwanci?

Gaskiya ban tabba samun ko daya daga cikin wani abu na tallafi ba.

Ko za ki bayyana mana wani abin da ya taba faruwa dake na farin ciki ko akasin haka a rayuwarki na wannan sana’ar?

Alhamdu lillah, ita dama sana’a ta gaji haka wata rana ka yi farin cikin wata ranan ka yi akasin haka. Na farin cikin shi ne yadda ina zaune a kira ni a ce ana son abu kuma wannan abu ban yi tunani za’a ce za’a saya a gurina ba amma sai a saya a guri lallai ina farin cikin sosai. Akasan haka kuwa shi ne a kira ka a ce ana son kaya sai an saya ko dai kun gama magana sai a ce an fasa. Ko kuma kaya da ka saya ya zo gurin sai an kawo ka ga bashi bane kai kuma ka riga ka gama magana da mai saya kuma su ce ba shi suke so ba, hakan yana bata min rai saboda mutane sun yadda da kai suke sayayya a gurinka, to bana ji dadi gaskiya.

Ya kike ganin yanayin tarbiya a wannan lokacin?

Gaskiyar magana tarbiya ta yi karanci a wanan lokaci. Muna wani zamani ne da sai dai mu ce Lahaula Walakuwati illa billah, sai dai mu ci gaba da addu’ar samun sauki wurin Allah. An yi sakace da tarbiyya koyarwar Manzon Sallallahu Alaihi Wasallama da kuma magabatanmu. To iyayenmu su kara lura da yara a ko ina suke, sannan su dinga yi musu addu’a saboda addu’ar iyaye tana da tasiri a gurin ‘ya’yansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Kara Kira Da Ayi Gwajin Kwayoyi Kafin Yin Aure – Marwa

Next Post

ECOWAS Ta Cire Takunkuman Da Ta Kakaba Wa Kasashen Nijar, Mali Da Guinea-Bissau 

Related

Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

3 months ago
Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
Tattaunawa

Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu

4 months ago
Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya
Tattaunawa

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

11 months ago
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u
Tattaunawa

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

11 months ago
Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
Tattaunawa

Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka

1 year ago
Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris
Tattaunawa

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

1 year ago
Next Post
ECOWAS

ECOWAS Ta Cire Takunkuman Da Ta Kakaba Wa Kasashen Nijar, Mali Da Guinea-Bissau 

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.