• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad

by Amina Bello Hamza
1 year ago
in Tattaunawa
0
A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashiyar ‘yar kasuwa mai fatan ganin ta dogara da kanta Fatima Sa’ad, ta yi wa Leadrship Hausa bayanin rayuwarta da yadda ta tsunduma a harkar kasuwanci, ci gaban ta samu da ma kalubalen da fuskata a harkar, in a cikin hakan ta ba wa iyaye shawarar su tashi tsaye wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance da wakiliyarmu Amina Bello Hamza.

Da farko za mu so ki bayyana mana sunanki

Sunana Fatima Sa’ad Aliyu. An haife ni a Tudun Jukun da ke Zariya, na yi karatuna tun daga Nursery har na kammala sikandirena, yanzu haka ina karatu a Nuhu Bamalli polytechnic Zariya.

Ko Malamar Na Da Aure?

A a ba ni da aure

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

Wace sana’a kike yi a halin yanzu?

Ina sayar da duk wani nau’i na sutura, (Hajibai, Atamfa, shadda, Leshi, yadi na maza da mata, jakunkuna, takalma, da dai sauran su. Sanan ina sana’ar hannu Hada jakunkuna, takalma, zannuwan gado, da fululunka kujeru da kuma sa’ar Aya da Riidi).

Menene ya baki sha’awar fara wannan sana’a?

To ni dai ba zance ga wani abu da ya ba ni sha’awa ba saboda tun ina firamare na nake sana’a irin ta dalibai a makarata irin su iloka, Aya, lokacin ban san ma mai zan yi da kudin ba kawai ni dai ina jin dadi in ji ana cewa ki bani abu kaza.

To daga baya ne da girma ya fara zuwa sanan na ji sha’awar ka san cewa kamar mamana saboda ita ‘yar kasuwa ce ba ta iya zama ba sana’a gaskiya.

Idan mutum na son fara wannan sana’ar wani abu zai tana da don samun cikakkiyar nasara?

To da farko de dole ne ya fara sa rai shi sa’ana zai yi kuma ya dauke ta da mahimmaci, saboda idan bai dauke ta da mahimmanci ba ba zai iya juriya akan ta ba, sanan sai jari ko da bashi da yawa in dai bai raina ba to lallai wata rana zai ga amfanin haka, cikakkiyar nasara ba’a samun ta haka dole sai ka hadu da jarabawa da kuma kalubale, to a nan za ka yi hakuri da juriya sai Allah ya taimake ka har ka kai ga cin nasara a rayuwarka.

Ta Yaya Kike Tallata Hajojinki?

Ina tallata hajata ne ta kafar sada zumunta (social media). Sannan duk inda zan shiga makaranta ce gidan biki kai koma ina ne to zan tallata hajata, haka ma cikin kawayena.

Kuma Alhamdu lillahi muna ganin alfanun haka.

Ko kin taba samun tallafin gwamnati ko wata hukuma a harkar kasuwanci?

Gaskiya ban tabba samun ko daya daga cikin wani abu na tallafi ba.

Ko za ki bayyana mana wani abin da ya taba faruwa dake na farin ciki ko akasin haka a rayuwarki na wannan sana’ar?

Alhamdu lillah, ita dama sana’a ta gaji haka wata rana ka yi farin cikin wata ranan ka yi akasin haka. Na farin cikin shi ne yadda ina zaune a kira ni a ce ana son abu kuma wannan abu ban yi tunani za’a ce za’a saya a gurina ba amma sai a saya a guri lallai ina farin cikin sosai. Akasan haka kuwa shi ne a kira ka a ce ana son kaya sai an saya ko dai kun gama magana sai a ce an fasa. Ko kuma kaya da ka saya ya zo gurin sai an kawo ka ga bashi bane kai kuma ka riga ka gama magana da mai saya kuma su ce ba shi suke so ba, hakan yana bata min rai saboda mutane sun yadda da kai suke sayayya a gurinka, to bana ji dadi gaskiya.

Ya kike ganin yanayin tarbiya a wannan lokacin?

Gaskiyar magana tarbiya ta yi karanci a wanan lokaci. Muna wani zamani ne da sai dai mu ce Lahaula Walakuwati illa billah, sai dai mu ci gaba da addu’ar samun sauki wurin Allah. An yi sakace da tarbiyya koyarwar Manzon Sallallahu Alaihi Wasallama da kuma magabatanmu. To iyayenmu su kara lura da yara a ko ina suke, sannan su dinga yi musu addu’a saboda addu’ar iyaye tana da tasiri a gurin ‘ya’yansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Kara Kira Da Ayi Gwajin Kwayoyi Kafin Yin Aure – Marwa

Next Post

ECOWAS Ta Cire Takunkuman Da Ta Kakaba Wa Kasashen Nijar, Mali Da Guinea-Bissau 

Related

Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
Tattaunawa

Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu

2 weeks ago
Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya
Tattaunawa

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

8 months ago
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u
Tattaunawa

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

8 months ago
Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
Tattaunawa

Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka

10 months ago
Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris
Tattaunawa

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

10 months ago
Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina
Tattaunawa

Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina

10 months ago
Next Post
ECOWAS

ECOWAS Ta Cire Takunkuman Da Ta Kakaba Wa Kasashen Nijar, Mali Da Guinea-Bissau 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.