ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad

by Amina Bello Hamza
3 years ago
Iyaye

Matashiyar ‘yar kasuwa mai fatan ganin ta dogara da kanta Fatima Sa’ad, ta yi wa Leadrship Hausa bayanin rayuwarta da yadda ta tsunduma a harkar kasuwanci, ci gaban ta samu da ma kalubalen da fuskata a harkar, in a cikin hakan ta ba wa iyaye shawarar su tashi tsaye wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance da wakiliyarmu Amina Bello Hamza.

Da farko za mu so ki bayyana mana sunanki

Sunana Fatima Sa’ad Aliyu. An haife ni a Tudun Jukun da ke Zariya, na yi karatuna tun daga Nursery har na kammala sikandirena, yanzu haka ina karatu a Nuhu Bamalli polytechnic Zariya.

ADVERTISEMENT

Ko Malamar Na Da Aure?

A a ba ni da aure

LABARAI MASU NASABA

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

Wace sana’a kike yi a halin yanzu?

Ina sayar da duk wani nau’i na sutura, (Hajibai, Atamfa, shadda, Leshi, yadi na maza da mata, jakunkuna, takalma, da dai sauran su. Sanan ina sana’ar hannu Hada jakunkuna, takalma, zannuwan gado, da fululunka kujeru da kuma sa’ar Aya da Riidi).

Menene ya baki sha’awar fara wannan sana’a?

To ni dai ba zance ga wani abu da ya ba ni sha’awa ba saboda tun ina firamare na nake sana’a irin ta dalibai a makarata irin su iloka, Aya, lokacin ban san ma mai zan yi da kudin ba kawai ni dai ina jin dadi in ji ana cewa ki bani abu kaza.

To daga baya ne da girma ya fara zuwa sanan na ji sha’awar ka san cewa kamar mamana saboda ita ‘yar kasuwa ce ba ta iya zama ba sana’a gaskiya.

Idan mutum na son fara wannan sana’ar wani abu zai tana da don samun cikakkiyar nasara?

To da farko de dole ne ya fara sa rai shi sa’ana zai yi kuma ya dauke ta da mahimmaci, saboda idan bai dauke ta da mahimmanci ba ba zai iya juriya akan ta ba, sanan sai jari ko da bashi da yawa in dai bai raina ba to lallai wata rana zai ga amfanin haka, cikakkiyar nasara ba’a samun ta haka dole sai ka hadu da jarabawa da kuma kalubale, to a nan za ka yi hakuri da juriya sai Allah ya taimake ka har ka kai ga cin nasara a rayuwarka.

Ta Yaya Kike Tallata Hajojinki?

Ina tallata hajata ne ta kafar sada zumunta (social media). Sannan duk inda zan shiga makaranta ce gidan biki kai koma ina ne to zan tallata hajata, haka ma cikin kawayena.

Kuma Alhamdu lillahi muna ganin alfanun haka.

Ko kin taba samun tallafin gwamnati ko wata hukuma a harkar kasuwanci?

Gaskiya ban tabba samun ko daya daga cikin wani abu na tallafi ba.

Ko za ki bayyana mana wani abin da ya taba faruwa dake na farin ciki ko akasin haka a rayuwarki na wannan sana’ar?

Alhamdu lillah, ita dama sana’a ta gaji haka wata rana ka yi farin cikin wata ranan ka yi akasin haka. Na farin cikin shi ne yadda ina zaune a kira ni a ce ana son abu kuma wannan abu ban yi tunani za’a ce za’a saya a gurina ba amma sai a saya a guri lallai ina farin cikin sosai. Akasan haka kuwa shi ne a kira ka a ce ana son kaya sai an saya ko dai kun gama magana sai a ce an fasa. Ko kuma kaya da ka saya ya zo gurin sai an kawo ka ga bashi bane kai kuma ka riga ka gama magana da mai saya kuma su ce ba shi suke so ba, hakan yana bata min rai saboda mutane sun yadda da kai suke sayayya a gurinka, to bana ji dadi gaskiya.

Ya kike ganin yanayin tarbiya a wannan lokacin?

Gaskiyar magana tarbiya ta yi karanci a wanan lokaci. Muna wani zamani ne da sai dai mu ce Lahaula Walakuwati illa billah, sai dai mu ci gaba da addu’ar samun sauki wurin Allah. An yi sakace da tarbiyya koyarwar Manzon Sallallahu Alaihi Wasallama da kuma magabatanmu. To iyayenmu su kara lura da yara a ko ina suke, sannan su dinga yi musu addu’a saboda addu’ar iyaye tana da tasiri a gurin ‘ya’yansu.

Iyaye
Amina Bello Hamza
+ postsBio
  • Amina Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-bello-hamza/
    Mazan Yanzu Ba Sa Son Matan Da Za Su Zame Masu Jidali – Zahra
  • Amina Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-bello-hamza/
    Duk Matakin Ilimin Bokon Mutum Bai Kamata Ya Yi Wasa Da Sana’a Ba – Ramatu Bello
  • Amina Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-bello-hamza/
    Yadda Ake Samosa
  • Amina Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-bello-hamza/
    Ina Da Burin Ganin Mata Sun Dogara Da Kansu A Harkokin Rayuwa – Lu’ayyat Mu’az

MASU ALAKA

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
Tattaunawa

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

August 28, 2026
Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Tattaunawa

Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

August 20, 2026
Nijeriya
Tattaunawa

2027: Shugaba Mai Gaskiya Da Hangen Nesa Nijeriya Ke Buƙata —Ahmad Shu’aibu

August 8, 2026
Next Post
ECOWAS

ECOWAS Ta Cire Takunkuman Da Ta Kakaba Wa Kasashen Nijar, Mali Da Guinea-Bissau 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.