• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Shirye Sin Take Ta Tsara Yarjeniyoyin Ciniki Cikin ’Yanci Da Karin Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
A Shirye Sin Take Ta Tsara Yarjeniyoyin Ciniki Cikin ’Yanci Da Karin Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maaikatar harkokin wajen Sin ta ce har kullum, kasar kan nace ga adawa da kariyar cinikayya, tare da nacewa ga inganta ci gaban duniya ta hanyar cinikayya da rage gibin dake akwai tsakanin manya da kananan kasashe. Kuma a shirye take ta tsara yarjeniyoyin ciniki cikin ’yanci da karin kasashe masu tasowa.

 

Kakakin maaikatar Mao Ning ce ta bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Alhamis.

  • Wang Yi Ya Yi Kira Ga Kasashe Mambobin BRICS Da Su Yi Hadin Gwiwar Shawo Kan Kalubalen Tsaro
  • Babban Sakataren Cibiyar ACBF Ya Yi Maraba Da Aniyar Kasar Sin Ta Tallafawa Noma Da Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi

Rahoton yanayin cinikayya a duniya na shekarar 2024 da hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) ta fitar a baya bayan nan, ya jaddada muhimmancin cinikayya wajen rage talauci da samar da ci gaba na bai daya, tare da bayyana cewa, tsananta kariyar cinikayya ka iya mayar da hannun agogo baya, ta fuskar rage gibin dake tsakanin masu hannu da shuni da masu karamin karfi, da shekaru 30. A cewar darakta janar ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala, karuwa da kyautatuwar harkokin cinikayya ka iya ba karin mutane da yankunan damar dunkulewa zuwa karfin tattalin arzikin duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

A cewar Mao Ning, kasar Sin ta kasance babbar mai bayar da gudunmuwa ga aiwatar da harkokin cinikayya cikin ’yanci. Ta ce yayin taron kolin dandalin tattauna hadin kan Sin da Afrika, shugaban Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarwarin hadin gwiwa 10, ciki har da hadin gwiwa domin inganta ci gaban cinikayya tare da sanar da fadada bude kofar kasuwar kasarsa da soke haraji kan wasu kayayyaki da suka cancanci biyan kaso 100 bisa 100 na haraji, wadanda suka fito daga kasashen Afrika mafiya rangwamen karfi, inda kasar Sin ta zama babbar kasa mai tasowa ta farko, kuma mai karfin tattalin arziki a duniya, da ta aiwatar da wannan shiri. (Faiza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Yi Kira Ga Kasashe Mambobin BRICS Da Su Yi Hadin Gwiwar Shawo Kan Kalubalen Tsaro

Next Post

Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar ‘Onga Taste The Millions Promo’

Related

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

41 minutes ago
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

18 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

19 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

20 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

21 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

22 hours ago
Next Post
Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar ‘Onga Taste The Millions Promo’

Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar 'Onga Taste The Millions Promo’

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.