• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Shirye Sin Take Ta Tsara Yarjeniyoyin Ciniki Cikin ’Yanci Da Karin Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Maaikatar harkokin wajen Sin ta ce har kullum, kasar kan nace ga adawa da kariyar cinikayya, tare da nacewa ga inganta ci gaban duniya ta hanyar cinikayya da rage gibin dake akwai tsakanin manya da kananan kasashe. Kuma a shirye take ta tsara yarjeniyoyin ciniki cikin ’yanci da karin kasashe masu tasowa.

 

Kakakin maaikatar Mao Ning ce ta bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Alhamis.

  • Wang Yi Ya Yi Kira Ga Kasashe Mambobin BRICS Da Su Yi Hadin Gwiwar Shawo Kan Kalubalen Tsaro
  • Babban Sakataren Cibiyar ACBF Ya Yi Maraba Da Aniyar Kasar Sin Ta Tallafawa Noma Da Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi

Rahoton yanayin cinikayya a duniya na shekarar 2024 da hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) ta fitar a baya bayan nan, ya jaddada muhimmancin cinikayya wajen rage talauci da samar da ci gaba na bai daya, tare da bayyana cewa, tsananta kariyar cinikayya ka iya mayar da hannun agogo baya, ta fuskar rage gibin dake tsakanin masu hannu da shuni da masu karamin karfi, da shekaru 30. A cewar darakta janar ta WTO Ngozi Okonjo-Iweala, karuwa da kyautatuwar harkokin cinikayya ka iya ba karin mutane da yankunan damar dunkulewa zuwa karfin tattalin arzikin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

A cewar Mao Ning, kasar Sin ta kasance babbar mai bayar da gudunmuwa ga aiwatar da harkokin cinikayya cikin ’yanci. Ta ce yayin taron kolin dandalin tattauna hadin kan Sin da Afrika, shugaban Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarwarin hadin gwiwa 10, ciki har da hadin gwiwa domin inganta ci gaban cinikayya tare da sanar da fadada bude kofar kasuwar kasarsa da soke haraji kan wasu kayayyaki da suka cancanci biyan kaso 100 bisa 100 na haraji, wadanda suka fito daga kasashen Afrika mafiya rangwamen karfi, inda kasar Sin ta zama babbar kasa mai tasowa ta farko, kuma mai karfin tattalin arziki a duniya, da ta aiwatar da wannan shiri. (Faiza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai
Daga Birnin Sin

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Next Post
Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar ‘Onga Taste The Millions Promo’

Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar 'Onga Taste The Millions Promo’

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.