• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Al'adu, Ra'ayi Riga, Ra'ayi Riga, Tarihi
0
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani al’amari mai cike da takaici da kusan kowa ya sani, makircin siyasa a Jihar Kano ya sake jefa babbar masarautar jihar cikin wani yanayi wanda ba ita kaɗai abin ya taɓa ba har da ma yankin Arewa.

Maido da Sanusi Lamido Sanusi a matsayin Sarkin Kano da Gwamna Abba Yusuf ya yi, tare da sauke wasu sarakuna biyar da gwamnatin da ta gabata ta naɗa, ya zama abin da al’umma ke ta tofa albarkacin bakinsu a kai game da halin da sarakunan gargajiya suka tsinci kansu a ciki yayin da suka shiga tsaka mai wuya a tsakiyar ɓangarancin siyasa.

  • Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano
  • Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari’ar Sarakunan Kano

Wannan labari mara daɗi ba lamari ne da ya sha bamban ba; alama ce ta wani yanayi mai tayar da hankali da ya addabi jihohi dabandaban a faɗin ƙasar nan.

Idan za mu iya tunawa, tsohon Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello ya tsige wani basaraken gargajiya mai daraja ta ɗaya, Ohimege Igu, na koton-Nkarfe, Alhaji Abdulrazaq Isa Koto.

Za mu kuma tuna cewa a shekarar 2022, sa’o’i 24 bayan hawansa mulki a matsayin Gwamnan Jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke ya sauke wasu sarakunan gargajiya uku da magajinsa, Adegboyega Oyetola ya naɗa.

Labarai Masu Nasaba

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Tun daga Kogi zuwa Osun, da kuma Kano, mun ga yadda sarakunan gargajiya ke rungume hannu suna kallo ana korar su bisa son zuciya na gwamnatocin da ke hawa karagar mulki, galibi a matsayin ramuwar gayya kan abin da suka yi na mubaya’a, ko kuma a matsayin hanyar da za a tabbatar da ƙara karfin mulki.

A ra’ayin wannan jaridar, wannan wasan siyasa mai ban mamaki da ake yi wa masarautun gargajiya ba wai kawai yana zubar da ƙimarsu ba ne har ma yana lalata tushen l’adun ƙasar nan da aka gada kaka da kakanni ne.

Ana son masarautun gargajiya su masu kula da ɗimbin tarihi da al’adun Nijeriya, waɗanda ke tattare da gyara ɗabi’u da al’adu da hikimomi waɗanda ake gadar wa ƴan baya.

Waɗannan masarautun sun kasance ababen girmamawa ne ba kawai a cikin al’ummominsu ba har ma a duk faɗin ƙasar nan.To sai dai idan suka zama ƴan amshin shata a wasannin siyasa na masu riƙe da madafun iko, to kwarjininsu da ikonsu yana matuƙar raguwa, kuma amanar da talakawan suka ba su tana shiga cikin haɗari.

Dole ne mu kula tare da killace masarautunmu na gargajiya daga rugujewa a sakamakon siyasar ɓangaranci. Dole ne a yi tir da kakkausar murya kan yadda wamnoni ke korar sarakunan gargajiya tare da mayar da su kan karaga bisa manufarsu ta siyasa.

Irin waɗannan abubuwa ba wai kawai suna zubar da mutuncin waɗannan masarautun ba ne, har ma suna haifar da saɓani da rashin zaman lafiya a tsakanin al’ummomin da suka daɗe suna dogaro da hikima da jagoranci na sarakunansu na gargajiya.

Duk da yake gaskiya ya kamata sarakunan gargajiya su nesanta kansu daga siyasar ɓangaranci, kuma su ci gaba da kasancewa iyayen ƙasa, kowa nasu ne, ya kamata aikinsu na masu kula da abubuwan da aka gada na gargajiya da samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummominsu ya kasance mara zargi.

Kamata ya yi a bar su, su sauke nauyin da ke kansu ba tare da tsoron fushi ko tsangwama ba daga ƴan siyasa ba.Ya kamata a lura da cewa, akwai ƙwararan dalilai na tsige sarakunan gargajiya, kamar samunsu da hannu wajen aikata laifuka, rashin biyayya, ko munanan ɗabi’u da ke barazana ga rayuwar al’ummarsu.

A irin waɗannan lokuta, dole ne a bi tsarin da ya dace, kuma matakin da za a ɗauka ya kamata ya dogara ne a kan ƙwararan hujjoji kuma a gudanar da shi ta hanyar tsarin doka, ba son rai na siyasa ba.

Al’amuran da suka faru a Sakkwato, inda gwamnan jihar ya sige hakimai 15 kan karagar mulki bisa zargin rashin biyayya, satar filaye, da taimakon rashin tsaro da kuma dakatar da wani basaraken gargajiya a Jihar Oyo bisa zargin alaƙa da masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, misali ne na matakan da suka dace da aka ɗauka domin tabbatar da kare mutuncin masarautun gargajiya da kare da muradun mutanen da suke yi wa hidima.

To sai dai kuma halin da ake ciki a Kano, inda ake ganin mayar da sarki ɗaya da tsige wasu daga muƙaminsa na siyasa ne kawai, ya sha bamban da abubuwan da ake ganin na ƙa’ida ne.

Irin haka kuma yana lalata kimar waɗannan cibiyoyi kuma yana haifar da ƙarin rarrabuwar kawuna da ɓacin rai a tsakanin al’ummomin da tuni suke kokawa da ƙalubalen rashin tsaro da tashe-tashen hankula na zamantakewar al’umma.

Lokaci ya yi da al’umma za su fahimci gagarumar gudunmawar da masarautun gargajiya za su iya bayarwa wajen samar da haɗin kai, da kiyaye al’adunmu, da magance matsalolin da suka addabi ƙasar nan.

Waɗannan cibiyoyi, idan aka mutunta su da kuma ba su ƙarfi, za su iya zama ƙawance mai ƙarfi a yaƙi da rashin tsaro, waɗanda za su zama ginshiƙan tattaunawanda warware rikice-rikice, da faɗaɗa ci gaban al’umma.

Domin samun nasarar wannan, dole ne mu sanya ƙarin kariya ga masarautunmu a cikin kundin tsarin mulkin ƙasa.

Dole ne a samar da sahihan tsaretsare na naɗawa da tsara wa’adin mulki, da tsige sarakunan gargajiya, tare da kawar da kai daga son zuciyar ƴan siyasa da tabbatar da cewa aikinsu ya kasance bisa maslahar al’ummarsu ba tsarin ɓangaranci ba.

Bugu da ƙuari, dole ne mu ƙarfafam asarautun gargajiya su rungumi aikin da ya dace a matsayin masu kula da al’adunmu na gargajiya da samar da zaman lafiya tare da nesantar siyasar ɓangaranci.

Ana iya samun nasarar hakan ta hanyar tabbatar da ɗorewar ilimin al’umma, da tattaunawa da haɓaka mutunta waɗannan cibiyoyi masu daraja.

Yayin da muke kai-komo a cikin sarqaqiyar yanayin siyasar qasarmu, ka da mu manta da ximbin kima da muhimmancin da masarautunmu na gargajiya suke da su.

Ta hanyar kiyaye mutuncinsu da kuma kare su daga mummunar tasirin siyasar ɓangaranci, za mu iya tabbatar da cewa waɗannanasarautun sun ci gaba da zama ginshiƙan samun kyakkyawan fata da kuma kwanciyar hankali ga zurriyyar da ake hayayyafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BayerokanoSarakunaSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Next Post

EFCC Ta Sanya Tukwici Ga Masu Fallasa Waɗanda Ke Wulaƙanta Naira

Related

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

2 days ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

4 days ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

1 week ago
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

1 week ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

1 week ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

1 week ago
Next Post
EFCC Ta Sanya Tukwici Ga Masu Fallasa  Waɗanda Ke Wulaƙanta Naira

EFCC Ta Sanya Tukwici Ga Masu Fallasa Waɗanda Ke Wulaƙanta Naira

LABARAI MASU NASABA

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

August 2, 2025
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.