• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Gwamna Dauda Ya Faɗa Wa Manazartan Harkokin Tsaro Kan Yaƙi Da Matsalar Tsaro A Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Abin Da Gwamna Dauda Ya Faɗa Wa Manazartan Harkokin Tsaro Kan Yaƙi Da Matsalar Tsaro A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunƙuri na kawo ƙarshen ta’addanci, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatin sa na haɗa kai da hukumomin tsaro da suka haɗa da Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) don magance matsalar rashin tsaro a Jihar Zamfara.

A ranar Larabar da ta gabata ne tawagar manyan jami’ai masu karatun harkar tsaro na sirri ta ƙasa (EIMC) 17/2024 da jami’an na Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa suka ziyarci Jihar Zamfara inda suka gana da Gwamna Dauda Lawal.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, taken taron shi ne “Ƙirƙirarriyar Basira ‘IA’, Tsaro da Haɓaka Tattalin Arziki A Afrika: Ƙalubale Da Samar Da Mafita” Mahalarta taron sun fito ne daga hukumomi daban-daban a ciki da wajen ƙasar nan.

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, taron ya baiwa mahalarta damar musayar ra’ayoyi da shawarwari kan batutuwa masu muhimmanci da mabambantan ra’ayoyi, wanda zai haifar da sakamako mai kyau.

gwamna

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Da yake jawabi ga jami’ai da mahalarta taron, Gwamna Lawal ya yaba wa cibiyar da ta zaɓi Jihar Zamfara domin gudanar da taron. “Shawarar ta dace ga wasu muhimman canje-canje da muke ƙoƙarin aiwatarwa. Kamar sauran sassan Nijeriya, Jihar mu tana da ɗimbin albarkatun ƙasa da na Ɗan’adam, waɗanda a matsayinsu na ginshiƙan ci gaban tattalin arziki, za su iya buɗe hanyoyin haɓaka tattalin arziki.

“Komawa kan maƙasudin taron tare da mai da hankali kan aikin Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, gami da sabbin aikace-aikacen fasaha na Ƙirƙirarriyar Basira don haɓaka fa’idojin ma’adanai da ke cikin jiharmu da kuma magance barazanar da ke tattare da mu, dole ne mu daidaita su. Sanin wannan, gwamnatina tana aiki tare da hukumomin tsaro da sauran abokan haɗin gwiwa don haɓaka ƙwarewa a fannin fasaha don magance matsalolinmu.

gwamna

“Saboda haka ina kira gare ku, mahalarta kwas ɗin, da ku yi tambayoyi da yawa tare da yin nazarin al’amuran da ke faruwa tare da samar mana da ingantattun shawarwari da suka dace da gwamnatin jiha don aiwatarwa. Idan har aka samu hakan, wannan ziyarar karatu za ta yi amfani matuƙa.”

Bugu da ƙari, Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa gwamnatin jihar Zamfara na haɗa kai da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile barazanar tsaro.

“Tun da muka karɓi mulki kimanin shekara guda da ta wuce, mun ɓullo da wasu matakai na musamman da suka haɗa da tarukan Majalisar Tsaron Jihohi na yau da kullum don duba yanayin tsaro, da fara tsarin aiwatar da shi, da kuma kafa Asusun Tallafa wa Tsaro na Jihar Zamfara.

“Har ila yau, mun tsaurara matakai inda muka aiwatar da dokar hana zirga-zirga a kan takamaiman ayyukan da ka iya taimaka wa rashin tsaro a cikin Jihar; Ƙaddamar da Dokar Zartarwa da ta haramta wa sarakunan gargajiya bayar da izinin haƙar ma’adinai a cikin ƙananan hukumomi goma sha huɗu na jihar, don mayar da martani ga ƙaƙƙarfan alaƙar da ke tsakanin ‘yan bindiga da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

“Sanya dokar ta-ɓaci a harkokin lafiya da ilimi don mu samar da ci gaba mai amfani ga jama’ar mu cikin gaggawa a waɗannan fannoni, tare da shinfiɗa turbar samar da gobe mai kyau ga al’ummar jihar mu; Samar da rundunar tsaro ta musamman ta Askarawan Zamfara domin taimaka wa jami’an tsaron da ke jihar wajen shawo kan matsalolin tsaro ya addab.

Tun farko a nata jawabin, Shugabar tawagar jami’an daga wannan cibiya ta koyon harkokin tsaro, Madam Patricia Edak, ta yaba wa Gwamna Dauda Lawal ne bisa irin ci gaban da ya samar wa jihar a mulkin sa.

Ta ce, “Mai girma Gwamna, mun zagaya jihar nan mun ga irin manya-manyan gyare-gyare da ci gaban da ka samar a wannan ɗan ƙanƙanin lokacin da ka yi a kan mulki. Gaskiyar magana, jihar Zamfara ta yi gagarumar sa’a na samun ka a matsayin Gwamna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaGwamna Dauda LawalJihar ZamfaraJihohiKwasNazariTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Muka Samar Da Cikakken Ci Gaba A Jami’ar Modibbo Adama Cikin Shekaru 5 – Farfesa Liman

Next Post

Tinubu Ya Taya Ministan Yaɗa Labarai Murnar Cika Shekaru 58

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

6 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

8 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

10 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

13 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

16 hours ago
Next Post
Malagi

Tinubu Ya Taya Ministan Yaɗa Labarai Murnar Cika Shekaru 58

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.