• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Gwamna Dauda Ya Faɗa Wa Manazartan Harkokin Tsaro Kan Yaƙi Da Matsalar Tsaro A Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Abin Da Gwamna Dauda Ya Faɗa Wa Manazartan Harkokin Tsaro Kan Yaƙi Da Matsalar Tsaro A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunƙuri na kawo ƙarshen ta’addanci, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatin sa na haɗa kai da hukumomin tsaro da suka haɗa da Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) don magance matsalar rashin tsaro a Jihar Zamfara.

A ranar Larabar da ta gabata ne tawagar manyan jami’ai masu karatun harkar tsaro na sirri ta ƙasa (EIMC) 17/2024 da jami’an na Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa suka ziyarci Jihar Zamfara inda suka gana da Gwamna Dauda Lawal.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, taken taron shi ne “Ƙirƙirarriyar Basira ‘IA’, Tsaro da Haɓaka Tattalin Arziki A Afrika: Ƙalubale Da Samar Da Mafita” Mahalarta taron sun fito ne daga hukumomi daban-daban a ciki da wajen ƙasar nan.

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, taron ya baiwa mahalarta damar musayar ra’ayoyi da shawarwari kan batutuwa masu muhimmanci da mabambantan ra’ayoyi, wanda zai haifar da sakamako mai kyau.

gwamna

Labarai Masu Nasaba

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Da yake jawabi ga jami’ai da mahalarta taron, Gwamna Lawal ya yaba wa cibiyar da ta zaɓi Jihar Zamfara domin gudanar da taron. “Shawarar ta dace ga wasu muhimman canje-canje da muke ƙoƙarin aiwatarwa. Kamar sauran sassan Nijeriya, Jihar mu tana da ɗimbin albarkatun ƙasa da na Ɗan’adam, waɗanda a matsayinsu na ginshiƙan ci gaban tattalin arziki, za su iya buɗe hanyoyin haɓaka tattalin arziki.

“Komawa kan maƙasudin taron tare da mai da hankali kan aikin Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, gami da sabbin aikace-aikacen fasaha na Ƙirƙirarriyar Basira don haɓaka fa’idojin ma’adanai da ke cikin jiharmu da kuma magance barazanar da ke tattare da mu, dole ne mu daidaita su. Sanin wannan, gwamnatina tana aiki tare da hukumomin tsaro da sauran abokan haɗin gwiwa don haɓaka ƙwarewa a fannin fasaha don magance matsalolinmu.

gwamna

“Saboda haka ina kira gare ku, mahalarta kwas ɗin, da ku yi tambayoyi da yawa tare da yin nazarin al’amuran da ke faruwa tare da samar mana da ingantattun shawarwari da suka dace da gwamnatin jiha don aiwatarwa. Idan har aka samu hakan, wannan ziyarar karatu za ta yi amfani matuƙa.”

Bugu da ƙari, Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa gwamnatin jihar Zamfara na haɗa kai da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile barazanar tsaro.

“Tun da muka karɓi mulki kimanin shekara guda da ta wuce, mun ɓullo da wasu matakai na musamman da suka haɗa da tarukan Majalisar Tsaron Jihohi na yau da kullum don duba yanayin tsaro, da fara tsarin aiwatar da shi, da kuma kafa Asusun Tallafa wa Tsaro na Jihar Zamfara.

“Har ila yau, mun tsaurara matakai inda muka aiwatar da dokar hana zirga-zirga a kan takamaiman ayyukan da ka iya taimaka wa rashin tsaro a cikin Jihar; Ƙaddamar da Dokar Zartarwa da ta haramta wa sarakunan gargajiya bayar da izinin haƙar ma’adinai a cikin ƙananan hukumomi goma sha huɗu na jihar, don mayar da martani ga ƙaƙƙarfan alaƙar da ke tsakanin ‘yan bindiga da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

“Sanya dokar ta-ɓaci a harkokin lafiya da ilimi don mu samar da ci gaba mai amfani ga jama’ar mu cikin gaggawa a waɗannan fannoni, tare da shinfiɗa turbar samar da gobe mai kyau ga al’ummar jihar mu; Samar da rundunar tsaro ta musamman ta Askarawan Zamfara domin taimaka wa jami’an tsaron da ke jihar wajen shawo kan matsalolin tsaro ya addab.

Tun farko a nata jawabin, Shugabar tawagar jami’an daga wannan cibiya ta koyon harkokin tsaro, Madam Patricia Edak, ta yaba wa Gwamna Dauda Lawal ne bisa irin ci gaban da ya samar wa jihar a mulkin sa.

Ta ce, “Mai girma Gwamna, mun zagaya jihar nan mun ga irin manya-manyan gyare-gyare da ci gaban da ka samar a wannan ɗan ƙanƙanin lokacin da ka yi a kan mulki. Gaskiyar magana, jihar Zamfara ta yi gagarumar sa’a na samun ka a matsayin Gwamna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaGwamna Dauda LawalJihar ZamfaraJihohiKwasNazariTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Muka Samar Da Cikakken Ci Gaba A Jami’ar Modibbo Adama Cikin Shekaru 5 – Farfesa Liman

Next Post

Tinubu Ya Taya Ministan Yaɗa Labarai Murnar Cika Shekaru 58

Related

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

5 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

6 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

7 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

8 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

9 hours ago
Next Post
Malagi

Tinubu Ya Taya Ministan Yaɗa Labarai Murnar Cika Shekaru 58

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.