ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Gwamna Dauda Ya Faɗa Wa Manazartan Harkokin Tsaro Kan Yaƙi Da Matsalar Tsaro A Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

A wani yunƙuri na kawo ƙarshen ta’addanci, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatin sa na haɗa kai da hukumomin tsaro da suka haɗa da Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) don magance matsalar rashin tsaro a Jihar Zamfara.

A ranar Larabar da ta gabata ne tawagar manyan jami’ai masu karatun harkar tsaro na sirri ta ƙasa (EIMC) 17/2024 da jami’an na Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa suka ziyarci Jihar Zamfara inda suka gana da Gwamna Dauda Lawal.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, taken taron shi ne “Ƙirƙirarriyar Basira ‘IA’, Tsaro da Haɓaka Tattalin Arziki A Afrika: Ƙalubale Da Samar Da Mafita” Mahalarta taron sun fito ne daga hukumomi daban-daban a ciki da wajen ƙasar nan.

ADVERTISEMENT
  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, taron ya baiwa mahalarta damar musayar ra’ayoyi da shawarwari kan batutuwa masu muhimmanci da mabambantan ra’ayoyi, wanda zai haifar da sakamako mai kyau.

gwamna

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Da yake jawabi ga jami’ai da mahalarta taron, Gwamna Lawal ya yaba wa cibiyar da ta zaɓi Jihar Zamfara domin gudanar da taron. “Shawarar ta dace ga wasu muhimman canje-canje da muke ƙoƙarin aiwatarwa. Kamar sauran sassan Nijeriya, Jihar mu tana da ɗimbin albarkatun ƙasa da na Ɗan’adam, waɗanda a matsayinsu na ginshiƙan ci gaban tattalin arziki, za su iya buɗe hanyoyin haɓaka tattalin arziki.

“Komawa kan maƙasudin taron tare da mai da hankali kan aikin Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, gami da sabbin aikace-aikacen fasaha na Ƙirƙirarriyar Basira don haɓaka fa’idojin ma’adanai da ke cikin jiharmu da kuma magance barazanar da ke tattare da mu, dole ne mu daidaita su. Sanin wannan, gwamnatina tana aiki tare da hukumomin tsaro da sauran abokan haɗin gwiwa don haɓaka ƙwarewa a fannin fasaha don magance matsalolinmu.

gwamna

“Saboda haka ina kira gare ku, mahalarta kwas ɗin, da ku yi tambayoyi da yawa tare da yin nazarin al’amuran da ke faruwa tare da samar mana da ingantattun shawarwari da suka dace da gwamnatin jiha don aiwatarwa. Idan har aka samu hakan, wannan ziyarar karatu za ta yi amfani matuƙa.”

Bugu da ƙari, Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa gwamnatin jihar Zamfara na haɗa kai da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile barazanar tsaro.

“Tun da muka karɓi mulki kimanin shekara guda da ta wuce, mun ɓullo da wasu matakai na musamman da suka haɗa da tarukan Majalisar Tsaron Jihohi na yau da kullum don duba yanayin tsaro, da fara tsarin aiwatar da shi, da kuma kafa Asusun Tallafa wa Tsaro na Jihar Zamfara.

“Har ila yau, mun tsaurara matakai inda muka aiwatar da dokar hana zirga-zirga a kan takamaiman ayyukan da ka iya taimaka wa rashin tsaro a cikin Jihar; Ƙaddamar da Dokar Zartarwa da ta haramta wa sarakunan gargajiya bayar da izinin haƙar ma’adinai a cikin ƙananan hukumomi goma sha huɗu na jihar, don mayar da martani ga ƙaƙƙarfan alaƙar da ke tsakanin ‘yan bindiga da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

“Sanya dokar ta-ɓaci a harkokin lafiya da ilimi don mu samar da ci gaba mai amfani ga jama’ar mu cikin gaggawa a waɗannan fannoni, tare da shinfiɗa turbar samar da gobe mai kyau ga al’ummar jihar mu; Samar da rundunar tsaro ta musamman ta Askarawan Zamfara domin taimaka wa jami’an tsaron da ke jihar wajen shawo kan matsalolin tsaro ya addab.

Tun farko a nata jawabin, Shugabar tawagar jami’an daga wannan cibiya ta koyon harkokin tsaro, Madam Patricia Edak, ta yaba wa Gwamna Dauda Lawal ne bisa irin ci gaban da ya samar wa jihar a mulkin sa.

Ta ce, “Mai girma Gwamna, mun zagaya jihar nan mun ga irin manya-manyan gyare-gyare da ci gaban da ka samar a wannan ɗan ƙanƙanin lokacin da ka yi a kan mulki. Gaskiyar magana, jihar Zamfara ta yi gagarumar sa’a na samun ka a matsayin Gwamna.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
Malagi

Tinubu Ya Taya Ministan Yaɗa Labarai Murnar Cika Shekaru 58

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.