ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
2 months ago
Kofin Duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da kasar Gabon a wasanta na gaba na neman tikitin zuwa gasar Kofin Duniya da za a buga a kasashen Amurka, Medico da Canada, wasan wanda za a buga a kasar Moroko ranar 13 ga watan Nuwamba zai zama sharar fage a wajen kasashen biyu, Nijeriya ta doke kasar Benin da ci 4-0 a wasan da suka buga a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom ranar Talata, wanda ya kasance wasa na karshe da kasar ta buga a cikin rukunin C inda ta kare a matsayi na biyu maki daya tsakaninta da Afirika Ta Kudu wadda ta kare a matsayi na 1.

 

Zakarun na Afrika har sau uku Nijeriya ta samu damar zuwa wasan Sili daya kwale bayan doke Jamhuriyar Benin, inda suka kare matsayi na biyu a rukuninsu na neman tikitin shiga gasar, ita kuma Gabon ta samu nasarar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasannin Play Off bayan nasarar da ta yi akan kasar Burundi da ci 2-0, nasarar da Ibory Coast ta samu a kan Kenya ne ya kara taimaka wa Gabon din kammala wasannin rukuni a matsayi na biyu a rukunin F.

ADVERTISEMENT
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

A daya bangaren kuma DR Congo ta lallasa Sudan da ci 1-0, inda ta zo ta biyu a bayan Senegal a rukunin B, yayin da Kamaru ta kare a matsayi na biyu a rukunin D, kasashen Nijeriya, Gabon, DR Congo da Kamaru ne suka samu damar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasan Sili daya Kwale, domin samun wadda za ta kara da wata kasa a Nahiyar Turai wajen ganin sun samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Za a gudanar da wasannin a kasar Morocco daga ranar 13 zuwa 16 ga watan Nuwamba, wanda zai kunshi Nijeriya da Gabon, sai kuma Kamaru da DR Congo, kasashen da suka yi nasara a wasan farko za su hadu da juna wasa na biyu domin fitar da zakara wanda zai buga wasa daya da wata kasa a Nahiyar Turai a watan Maris na shekarar 2026, dukkan wasannin za su kasance haduwa daya, sannan kuma za a iya karin mintuna 20 idan bukatar hakan ta taso (Edtra Time), ana sa ran hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF ta tabbatar da birane da wuraren da za su karbi bakuncin gasar a cikin kwanaki masu zuwa.

 

Yayin da kasashe 9 ne daga Afirika zuwa yanzu suka samu nasarar zuwa gasar Kofin Duniya, wasan na share fage na iya zama wata hanya da Afirika za ta samu karin wakilai daga Nahiyar wadanda za su samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya wadda kasashe 48 za su buga a shekarar 2026.

 

wasan na badi zai kasance Kofin Duniya na farko da kasashe fiye da 40 za su buga, kuma za a gudanar da shi a kasashe uku da suka hada da Amurka, Medico da Canada, a takaice Nijeriya na bukatar samun nasara a wasanni 3 da za ta buga a jere kafin samun damar zuwa gasar Kofin Duniya ta shekarar 2026.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal
Wasanni

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco
Wasanni

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey
Wasanni

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Next Post
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga 'Yan Bindiga A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.