• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
3 weeks ago
Kofin Duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da kasar Gabon a wasanta na gaba na neman tikitin zuwa gasar Kofin Duniya da za a buga a kasashen Amurka, Medico da Canada, wasan wanda za a buga a kasar Moroko ranar 13 ga watan Nuwamba zai zama sharar fage a wajen kasashen biyu, Nijeriya ta doke kasar Benin da ci 4-0 a wasan da suka buga a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom ranar Talata, wanda ya kasance wasa na karshe da kasar ta buga a cikin rukunin C inda ta kare a matsayi na biyu maki daya tsakaninta da Afirika Ta Kudu wadda ta kare a matsayi na 1.

 

Zakarun na Afrika har sau uku Nijeriya ta samu damar zuwa wasan Sili daya kwale bayan doke Jamhuriyar Benin, inda suka kare matsayi na biyu a rukuninsu na neman tikitin shiga gasar, ita kuma Gabon ta samu nasarar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasannin Play Off bayan nasarar da ta yi akan kasar Burundi da ci 2-0, nasarar da Ibory Coast ta samu a kan Kenya ne ya kara taimaka wa Gabon din kammala wasannin rukuni a matsayi na biyu a rukunin F.

  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

A daya bangaren kuma DR Congo ta lallasa Sudan da ci 1-0, inda ta zo ta biyu a bayan Senegal a rukunin B, yayin da Kamaru ta kare a matsayi na biyu a rukunin D, kasashen Nijeriya, Gabon, DR Congo da Kamaru ne suka samu damar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasan Sili daya Kwale, domin samun wadda za ta kara da wata kasa a Nahiyar Turai wajen ganin sun samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Za a gudanar da wasannin a kasar Morocco daga ranar 13 zuwa 16 ga watan Nuwamba, wanda zai kunshi Nijeriya da Gabon, sai kuma Kamaru da DR Congo, kasashen da suka yi nasara a wasan farko za su hadu da juna wasa na biyu domin fitar da zakara wanda zai buga wasa daya da wata kasa a Nahiyar Turai a watan Maris na shekarar 2026, dukkan wasannin za su kasance haduwa daya, sannan kuma za a iya karin mintuna 20 idan bukatar hakan ta taso (Edtra Time), ana sa ran hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF ta tabbatar da birane da wuraren da za su karbi bakuncin gasar a cikin kwanaki masu zuwa.

 

Yayin da kasashe 9 ne daga Afirika zuwa yanzu suka samu nasarar zuwa gasar Kofin Duniya, wasan na share fage na iya zama wata hanya da Afirika za ta samu karin wakilai daga Nahiyar wadanda za su samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya wadda kasashe 48 za su buga a shekarar 2026.

 

wasan na badi zai kasance Kofin Duniya na farko da kasashe fiye da 40 za su buga, kuma za a gudanar da shi a kasashe uku da suka hada da Amurka, Medico da Canada, a takaice Nijeriya na bukatar samun nasara a wasanni 3 da za ta buga a jere kafin samun damar zuwa gasar Kofin Duniya ta shekarar 2026.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko
Wasanni

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax
Wasanni

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Next Post
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga 'Yan Bindiga A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.