• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

byAbubakar Abba
2 years ago
Rani

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Nan da ‘yan kwanaki kadan za a fara yin noman rani na alkama, musamman a Jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Bauchi, Taraba, Kebbi, Jigawa, Sokoto, Gombe da sauransu.

Tsohon Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma na Jihar Gombe, kuma guda cikin manyan manoma, Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya bayyana cewa, manoman da suka yi shuka bayan ranar 15 ga watan Nuwamba, za su iya samun matsala ko tangarda a gonakinsu.

  • Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
  • GORON JUMA’A

 Sannan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, da ta tabbatar tana tallafa wa manoman alkama a kan lokaci, inda ya yi nuni da cewa, dabi’ar raba wa manona kayan aikin noma a makare ne ke jawo wa manoman kasar nan rashin samun amfani mai yawa bayan sun yi girbi.

Sai dai, wasu kwararru a fannin noman alkamar sun bai wa manoman kwarin guiwar cewa, za su iya yin shuka daga ranar 15 ga watan Nuwamba zuwa ranar 15 ga watan Disamba.

Kazalika, sun bayyana cewa; wadanda suke son su samu girbi mai yawa, za su iya yin shuka a makon farko na watan Nuwamba, ganin cewa alkama ta fi bukatar yanayin sanyi.

Daya daga cikin kwararru a wannan fanni kuma shugaban kungiyar masu sarrafa wa da kasuwancin alkama na kasa, Kwamanda Sojin Sama, mai ritaya Shuaibu Hamza ya sanar da cewa, kungiyar ta ware akalla kadada 77,000 domin yin noman alkama na rani.

Ya kara da cewa, a Jihar Neja akalla akwai kadadar yin noma kimanin 40,000, inda ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu manoman nata su kimanin 20,000 ne suka yi rijista, domin fara yin noman wannan alkama na rani.

Bugu da kari, a mako biyu da suka gabata ne, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya za ta noma kimanin kadada 70,000 a jihohin kasar nan da ke yin noman alkama, wadda ake sa ran za a samu girbin da ya kai na tan 875,000 domin adanawa.

Abubakar ya kara cewa, za a ware kadada 40,000 a Jihar Jigawa, sauran kadada 30,000 kuma za a raba su ga sauran jihohin da ke noman alkamar.

Wannan yana nuna cewa, Jihar Jigawa ita ce ta fi samun kaso mafi yawa, sakamakon jajircewar da take da shi a wannan fanni na noman alkamar, inda ta yi kokarin ware har kimanin kadada 40,000.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version