• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Nan da ‘yan kwanaki kadan za a fara yin noman rani na alkama, musamman a Jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Bauchi, Taraba, Kebbi, Jigawa, Sokoto, Gombe da sauransu.

Tsohon Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma na Jihar Gombe, kuma guda cikin manyan manoma, Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya bayyana cewa, manoman da suka yi shuka bayan ranar 15 ga watan Nuwamba, za su iya samun matsala ko tangarda a gonakinsu.

  • Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
  • GORON JUMA’A

 Sannan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, da ta tabbatar tana tallafa wa manoman alkama a kan lokaci, inda ya yi nuni da cewa, dabi’ar raba wa manona kayan aikin noma a makare ne ke jawo wa manoman kasar nan rashin samun amfani mai yawa bayan sun yi girbi.

Sai dai, wasu kwararru a fannin noman alkamar sun bai wa manoman kwarin guiwar cewa, za su iya yin shuka daga ranar 15 ga watan Nuwamba zuwa ranar 15 ga watan Disamba.

Kazalika, sun bayyana cewa; wadanda suke son su samu girbi mai yawa, za su iya yin shuka a makon farko na watan Nuwamba, ganin cewa alkama ta fi bukatar yanayin sanyi.

Daya daga cikin kwararru a wannan fanni kuma shugaban kungiyar masu sarrafa wa da kasuwancin alkama na kasa, Kwamanda Sojin Sama, mai ritaya Shuaibu Hamza ya sanar da cewa, kungiyar ta ware akalla kadada 77,000 domin yin noman alkama na rani.

Ya kara da cewa, a Jihar Neja akalla akwai kadadar yin noma kimanin 40,000, inda ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu manoman nata su kimanin 20,000 ne suka yi rijista, domin fara yin noman wannan alkama na rani.

Bugu da kari, a mako biyu da suka gabata ne, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya za ta noma kimanin kadada 70,000 a jihohin kasar nan da ke yin noman alkama, wadda ake sa ran za a samu girbin da ya kai na tan 875,000 domin adanawa.

Abubakar ya kara cewa, za a ware kadada 40,000 a Jihar Jigawa, sauran kadada 30,000 kuma za a raba su ga sauran jihohin da ke noman alkamar.

Wannan yana nuna cewa, Jihar Jigawa ita ce ta fi samun kaso mafi yawa, sakamakon jajircewar da take da shi a wannan fanni na noman alkamar, inda ta yi kokarin ware har kimanin kadada 40,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Za Ta Biya Ma’aikata Sama Da 16,000 Alawus Daga Kasafin Naira Biliyan 18 Da Aka Ware Mata – Yakubu

Next Post

Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

9 hours ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

19 hours ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 day ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

3 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

1 week ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

1 week ago
Next Post
Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

LABARAI MASU NASABA

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

June 22, 2025
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

June 22, 2025
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

June 22, 2025
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

June 22, 2025
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.