• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

by Abubakar Abba
2 years ago
Rani

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Nan da ‘yan kwanaki kadan za a fara yin noman rani na alkama, musamman a Jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Bauchi, Taraba, Kebbi, Jigawa, Sokoto, Gombe da sauransu.

Tsohon Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma na Jihar Gombe, kuma guda cikin manyan manoma, Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya bayyana cewa, manoman da suka yi shuka bayan ranar 15 ga watan Nuwamba, za su iya samun matsala ko tangarda a gonakinsu.

  • Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
  • GORON JUMA’A

 Sannan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, da ta tabbatar tana tallafa wa manoman alkama a kan lokaci, inda ya yi nuni da cewa, dabi’ar raba wa manona kayan aikin noma a makare ne ke jawo wa manoman kasar nan rashin samun amfani mai yawa bayan sun yi girbi.

Sai dai, wasu kwararru a fannin noman alkamar sun bai wa manoman kwarin guiwar cewa, za su iya yin shuka daga ranar 15 ga watan Nuwamba zuwa ranar 15 ga watan Disamba.

Kazalika, sun bayyana cewa; wadanda suke son su samu girbi mai yawa, za su iya yin shuka a makon farko na watan Nuwamba, ganin cewa alkama ta fi bukatar yanayin sanyi.

Daya daga cikin kwararru a wannan fanni kuma shugaban kungiyar masu sarrafa wa da kasuwancin alkama na kasa, Kwamanda Sojin Sama, mai ritaya Shuaibu Hamza ya sanar da cewa, kungiyar ta ware akalla kadada 77,000 domin yin noman alkama na rani.

Ya kara da cewa, a Jihar Neja akalla akwai kadadar yin noma kimanin 40,000, inda ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu manoman nata su kimanin 20,000 ne suka yi rijista, domin fara yin noman wannan alkama na rani.

Bugu da kari, a mako biyu da suka gabata ne, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya za ta noma kimanin kadada 70,000 a jihohin kasar nan da ke yin noman alkama, wadda ake sa ran za a samu girbin da ya kai na tan 875,000 domin adanawa.

Abubakar ya kara cewa, za a ware kadada 40,000 a Jihar Jigawa, sauran kadada 30,000 kuma za a raba su ga sauran jihohin da ke noman alkamar.

Wannan yana nuna cewa, Jihar Jigawa ita ce ta fi samun kaso mafi yawa, sakamakon jajircewar da take da shi a wannan fanni na noman alkamar, inda ta yi kokarin ware har kimanin kadada 40,000.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.