ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Farashin Kayan Masarufi Ya Fadi Warwas A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Masarufi

Sakamakon sabon tsarin da babban bankin Nijeriya CBN na sauya  takardun kudi na naira 1,000 da naira 500 da kuma naira 200 ya jefa ‘yan kasuwa a cikin tsaka-maiwuya, inda suke ci gaba da koka wa, kan asarar da  karancin sabbin kudin suka janyo wa sana’o’insu.

Har ila yau, rahotannin sun bayyana cewa, hakan ya kuma janyo faduwar farashin kayan masarufi a kasuwanni sakamakon karancin takardun kudaden a sassan kasar.

  • NIS Ta Yi Wa Jami’ai Sama 60 Karin Girma
  • Matsafa Sun Kashe Tare Da Cire Sassan Jikin Wani Dalibi A Adamawa

Kusan wannan matsalar ta karade kowanne fannin tun daga fannin hatsi da kuma dabbobi.

ADVERTISEMENT

Rahotanni sun bayyana cewa, farashin hatsi da sauran kayan abinci sun fadi warwas  a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, inda dole ta sa ’yan kasuwar suka fitar da farashin kaya iri biyu farashin mai biya da tsabar kudi daban, na mai biya ta tura kudi.

A kasuwar ta Dawanau, bayanai sun nuna cewa,  babban buhun masara da ake sayarwa naira 22,000 a makon jiya ya koma naira 14,000 da tsabar kudi, ko kuma naira 18,000 ga mai biya yin turin kudi.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Bugu da kari,  babban buhun gero da ke naira   25,000 a makon da ya wuce kuma ya koma naira 15,000 da tsabar kudi, ko naira 18,000 ga mai tura kudi,  inda kuma buhun shinkafa mai buntu mai nauyin 100 kilo  kuma ya koma naira 13,000 daga naira 23,000 da aka sayar a satin da ya gabata.

Wasu daga cikin masu hada-hadar hatsi a kasuwar sun bayyana cewa, a kan dole suke sayar da kaya, ko da faduwa za su yi don su samu abin da za su kula da iyalansu.

A cewarsu, rashin takardun kudi  ya sa kaya sun karye, ko ma ta wace hanya za a biya.

A jihar Kano a kasuwar kayan gwari ta ‘yankaba kuma, kwandon tumatir da ke naira 8,500 a makon jiya ya koma naira 4,000 saboda rashin ciniki.

A kasuwannin Jos da ke jihar Filato kuma farashin dankali, dankalin taurawa da sauran kayan gwari sun fadi  warwas, inda  kasuwar Farin Gada da ke Jos, kwandon tumatir da a baya ake sayarwa naira 1,500 zuwa naira 2,000 ya wuce ya koma naira I,  700.

Hakazalika, a kasuwar Maikatako, wadda ta yi fice wajen kasuwancin dankalin turawa a karamar hukumar Bokkos, farashin dankali ya fadi warwas, buhu mai nauyin kilo 50 na dankali ya koma naira 6,500 daga  farashinsa na naira 10,000.

A cewar wasu kananan manoma, mu ne muka fi shiga cikin matsala a wannan yanayi, inda suka kara da cewa, a makon da ya gabata a kasuwar kauyen Jamari an sayar da buhu mai nauyin kilo 100 na gero naira 7,000 sabanin naira 20,000 da ake sayarawa a baya.

A bangaren Masara ta koma naira 8,000-naira 10,000 amma kusan babu mai saya; Wake ya koma naira 19,000 daga naira 40,000; abin gwanin ban tausayi, kusan babu wanda bai shafa ba, saboda rashin takardun kudi.

Har ila yau, karancin kudin  ta sa rashin ciniki a kasuwar Alaba Rago da ke Jihar Legas, inda ’yan kasuwa ke ta korafi kan gazawar abokan cinikayya wajen samun tsabar kudi don yin sayayya.

A cewar wasu masu sana’ar sayar da kajin da aka sayar naira 10,000 a watan disamba da farkon watan janairu sun koma naira 6000, amma duk da haka babu mai saye.

Wasu ’yan kasuwa a kauyen Oke-Aro da ke kan iyakar jihohin Legas da Ogun sun bayyana irin asarar da suka tafka sakamakon rashin takardun kudaden.

Hakazalika, masu sana’ar sayar da kayan gwari a kasuwar Agbado don sayarwa a Oke-Aro ta bayyana cewa farashin kayan ba su canza ba, amma matsalar ita ce tashin farashin abin hawa, inda wasu tun da aka fara karancin takardun ba ya samun ciniki sosai.

A Jihar Kwara, wata ’yar kasuwa mai sayar da waken suya a  karamar hukumar   Kaiama, mai suna Amina ta ce lamarin ya sa ba su da zabi sai dai su koma su zauna a gida.

Wata mai sayar da hatsi mai suna Maimuna a Kaiama, ta ce ta bar sana’ar a halin yanzu saboda rashin uwar kudi  da kuma abin kula da  kanta.

A cewar wata  mai shinkafa da wake, Salamat, a Kasuwar Mandate da ke Ilorin ta ce duk da cewa ba asara suke yi a kayan da suke sayarwa ba, matsalar ta rage yanayin cininkinsu da ma harkar hatsi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Benzema Da Mbappe Da Messi Suna Takarar Gwarzon Dan Kwallon FIFA

Benzema Da Mbappe Da Messi Suna Takarar Gwarzon Dan Kwallon FIFA

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.