ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Farashin Kayan Masarufi Ya Fadi Warwas A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Masarufi

Sakamakon sabon tsarin da babban bankin Nijeriya CBN na sauya  takardun kudi na naira 1,000 da naira 500 da kuma naira 200 ya jefa ‘yan kasuwa a cikin tsaka-maiwuya, inda suke ci gaba da koka wa, kan asarar da  karancin sabbin kudin suka janyo wa sana’o’insu.

Har ila yau, rahotannin sun bayyana cewa, hakan ya kuma janyo faduwar farashin kayan masarufi a kasuwanni sakamakon karancin takardun kudaden a sassan kasar.

  • NIS Ta Yi Wa Jami’ai Sama 60 Karin Girma
  • Matsafa Sun Kashe Tare Da Cire Sassan Jikin Wani Dalibi A Adamawa

Kusan wannan matsalar ta karade kowanne fannin tun daga fannin hatsi da kuma dabbobi.

ADVERTISEMENT

Rahotanni sun bayyana cewa, farashin hatsi da sauran kayan abinci sun fadi warwas  a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, inda dole ta sa ’yan kasuwar suka fitar da farashin kaya iri biyu farashin mai biya da tsabar kudi daban, na mai biya ta tura kudi.

A kasuwar ta Dawanau, bayanai sun nuna cewa,  babban buhun masara da ake sayarwa naira 22,000 a makon jiya ya koma naira 14,000 da tsabar kudi, ko kuma naira 18,000 ga mai biya yin turin kudi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Bugu da kari,  babban buhun gero da ke naira   25,000 a makon da ya wuce kuma ya koma naira 15,000 da tsabar kudi, ko naira 18,000 ga mai tura kudi,  inda kuma buhun shinkafa mai buntu mai nauyin 100 kilo  kuma ya koma naira 13,000 daga naira 23,000 da aka sayar a satin da ya gabata.

Wasu daga cikin masu hada-hadar hatsi a kasuwar sun bayyana cewa, a kan dole suke sayar da kaya, ko da faduwa za su yi don su samu abin da za su kula da iyalansu.

A cewarsu, rashin takardun kudi  ya sa kaya sun karye, ko ma ta wace hanya za a biya.

A jihar Kano a kasuwar kayan gwari ta ‘yankaba kuma, kwandon tumatir da ke naira 8,500 a makon jiya ya koma naira 4,000 saboda rashin ciniki.

A kasuwannin Jos da ke jihar Filato kuma farashin dankali, dankalin taurawa da sauran kayan gwari sun fadi  warwas, inda  kasuwar Farin Gada da ke Jos, kwandon tumatir da a baya ake sayarwa naira 1,500 zuwa naira 2,000 ya wuce ya koma naira I,  700.

Hakazalika, a kasuwar Maikatako, wadda ta yi fice wajen kasuwancin dankalin turawa a karamar hukumar Bokkos, farashin dankali ya fadi warwas, buhu mai nauyin kilo 50 na dankali ya koma naira 6,500 daga  farashinsa na naira 10,000.

A cewar wasu kananan manoma, mu ne muka fi shiga cikin matsala a wannan yanayi, inda suka kara da cewa, a makon da ya gabata a kasuwar kauyen Jamari an sayar da buhu mai nauyin kilo 100 na gero naira 7,000 sabanin naira 20,000 da ake sayarawa a baya.

A bangaren Masara ta koma naira 8,000-naira 10,000 amma kusan babu mai saya; Wake ya koma naira 19,000 daga naira 40,000; abin gwanin ban tausayi, kusan babu wanda bai shafa ba, saboda rashin takardun kudi.

Har ila yau, karancin kudin  ta sa rashin ciniki a kasuwar Alaba Rago da ke Jihar Legas, inda ’yan kasuwa ke ta korafi kan gazawar abokan cinikayya wajen samun tsabar kudi don yin sayayya.

A cewar wasu masu sana’ar sayar da kajin da aka sayar naira 10,000 a watan disamba da farkon watan janairu sun koma naira 6000, amma duk da haka babu mai saye.

Wasu ’yan kasuwa a kauyen Oke-Aro da ke kan iyakar jihohin Legas da Ogun sun bayyana irin asarar da suka tafka sakamakon rashin takardun kudaden.

Hakazalika, masu sana’ar sayar da kayan gwari a kasuwar Agbado don sayarwa a Oke-Aro ta bayyana cewa farashin kayan ba su canza ba, amma matsalar ita ce tashin farashin abin hawa, inda wasu tun da aka fara karancin takardun ba ya samun ciniki sosai.

A Jihar Kwara, wata ’yar kasuwa mai sayar da waken suya a  karamar hukumar   Kaiama, mai suna Amina ta ce lamarin ya sa ba su da zabi sai dai su koma su zauna a gida.

Wata mai sayar da hatsi mai suna Maimuna a Kaiama, ta ce ta bar sana’ar a halin yanzu saboda rashin uwar kudi  da kuma abin kula da  kanta.

A cewar wata  mai shinkafa da wake, Salamat, a Kasuwar Mandate da ke Ilorin ta ce duk da cewa ba asara suke yi a kayan da suke sayarwa ba, matsalar ta rage yanayin cininkinsu da ma harkar hatsi.

Masarufi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Benzema Da Mbappe Da Messi Suna Takarar Gwarzon Dan Kwallon FIFA

Benzema Da Mbappe Da Messi Suna Takarar Gwarzon Dan Kwallon FIFA

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.