ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Ilimi

Fernando Reimers, wanda Daraktan ilimi ne a Jami’ar Harbard, sannan kuma mamba ne a hukumar UNESCO; a kan al’amuran da suka shafi fannin ilimi da kuma ci gabansa, an jiyo shi a wata tattauna da ya yi a CNBC yana cewa, muddin ba a tsaya an yi gyara a kan al’amuran da suka shafi ilimi ba, ko shakka babu akwai matsala a nan gaba.

Sai dai kuma, Bankin Duniya ya bayyana cewa; don mutum yana zuwa makaranta, ba shi ne yake nuna cewa; yana koyo ba (2019). Misali, kamar wanda ya karanta bayanin Likita ne ko kuma ya yarda cewa; mota za ta rika daukar fasinja, su ne dabarun abin da yawancin yara ba su samu damar sani ba.

  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Me yasa ilimi yake da muhimmanci? Dabaru, ilimi da kuma kware ta mutum, ana samun su ne ta hanyar ilimi. Wani binciken da Bankin Duniya ya sa aka yi a shekarar (2018) ya nuna cewa; kashi 56 na yaran da aka haifa a duniya, na iya asaar kudaden da suka samu wadanda za su iya taimaka musu wajen tafiyar da rayuwarsu. Dalili kuwa shi ne, gwamnatocinsu ba su zuba jari an kula da lafiya, ilimi da kuma irin wureren ayyukan da za su iya yi a nan gaba ba.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda Bankin duniyar ya ce, a shekarar (2019), an samu matsalar koyo ne saboda yawancin makarantu a kasashe daban-daban na hannu baka- hannu kwarya, wadanda ba su da alkalumman wadanda suke karatu da wadanda ba sa yi. Shi yasa ba za su iya yin wani abu ba dangane da hakan.

Dalili kuwa, ba a san irin bukatun da ake da su ba na lamarin da ya shafi ayyuka, matsalar ita ce makarantu da Malaman makaranta, akwai bukatar su koya musu bangaren da ya shafi rubutu da karatu. 

LABARAI MASU NASABA

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Kazalika, dalibai su kasance suna iya yin bayani a kan abin da suka fahimta na abin da aka koya musu, sannan su rika bayar da shawarwari, su kasance za su iya yin wani abu ta kirkira, su yi mu’amala da wasu ba tare da wata matsala ba, su ba da hadin kai, su kasance suna iya yin abin da ake so su yi.

Idan har aka samu damar magance wadannan matsaloli da aka ambata a sama tare kuma da tabbatar hanyoyin da ake bi koyarwa, ta haka za a iya samun gyaran da ake bukata. 

Bankin duniya a shekarar (2019) ya ce, ana fara samun sauyi ne daga Malaman makaranta; wadanda suka san abin da suke yi da kuma irin salon da ake amfani da shi wajen koyarwa. Bugu da kari kuma, ya kamata masana ilimi su yi amfani da irin ci gaban da fasaha ta kawo a wannan fanni na koyarwa.

Wasu Abubuwa Da Suka Shafi Ilimi A Duniya 

Kashi 88 na yara mata da kuma kashi 91 na yara maza, suna da ilimin Firamare, sai dai kuma mata da dama na samun ilimi mai zurfi fiye da maza, (World Economic Forum, 2019). 

A shekarar 2020, yawancin wadanda suka kammala karatun Firamare a fadin duniya baki-daya, kashi  90.14 cikin 100 ne, (UNESCO, 2021e). 

A cikin shekarar, an samu raguwar wadanda suka kammala karatun Sakandaren da kashi 77 cikin 100, (UNESCO, 2021d).

Haka nan ma, wadanda suka yi makarantar yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, kashi 86 ne cikin 100, (UNESCO, 2021c).

Wadanda suka yi yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, sun zarce kashi 83.3 cikin 100, yayin da su kuma maza suka kasance kashi 90 cikin 100, (UNESCO, 2021a; UNESCO, 2021b).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya
Ilimi

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Next Post
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.