ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Ilimi

Fernando Reimers, wanda Daraktan ilimi ne a Jami’ar Harbard, sannan kuma mamba ne a hukumar UNESCO; a kan al’amuran da suka shafi fannin ilimi da kuma ci gabansa, an jiyo shi a wata tattauna da ya yi a CNBC yana cewa, muddin ba a tsaya an yi gyara a kan al’amuran da suka shafi ilimi ba, ko shakka babu akwai matsala a nan gaba.

Sai dai kuma, Bankin Duniya ya bayyana cewa; don mutum yana zuwa makaranta, ba shi ne yake nuna cewa; yana koyo ba (2019). Misali, kamar wanda ya karanta bayanin Likita ne ko kuma ya yarda cewa; mota za ta rika daukar fasinja, su ne dabarun abin da yawancin yara ba su samu damar sani ba.

  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Me yasa ilimi yake da muhimmanci? Dabaru, ilimi da kuma kware ta mutum, ana samun su ne ta hanyar ilimi. Wani binciken da Bankin Duniya ya sa aka yi a shekarar (2018) ya nuna cewa; kashi 56 na yaran da aka haifa a duniya, na iya asaar kudaden da suka samu wadanda za su iya taimaka musu wajen tafiyar da rayuwarsu. Dalili kuwa shi ne, gwamnatocinsu ba su zuba jari an kula da lafiya, ilimi da kuma irin wureren ayyukan da za su iya yi a nan gaba ba.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda Bankin duniyar ya ce, a shekarar (2019), an samu matsalar koyo ne saboda yawancin makarantu a kasashe daban-daban na hannu baka- hannu kwarya, wadanda ba su da alkalumman wadanda suke karatu da wadanda ba sa yi. Shi yasa ba za su iya yin wani abu ba dangane da hakan.

Dalili kuwa, ba a san irin bukatun da ake da su ba na lamarin da ya shafi ayyuka, matsalar ita ce makarantu da Malaman makaranta, akwai bukatar su koya musu bangaren da ya shafi rubutu da karatu. 

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Kazalika, dalibai su kasance suna iya yin bayani a kan abin da suka fahimta na abin da aka koya musu, sannan su rika bayar da shawarwari, su kasance za su iya yin wani abu ta kirkira, su yi mu’amala da wasu ba tare da wata matsala ba, su ba da hadin kai, su kasance suna iya yin abin da ake so su yi.

Idan har aka samu damar magance wadannan matsaloli da aka ambata a sama tare kuma da tabbatar hanyoyin da ake bi koyarwa, ta haka za a iya samun gyaran da ake bukata. 

Bankin duniya a shekarar (2019) ya ce, ana fara samun sauyi ne daga Malaman makaranta; wadanda suka san abin da suke yi da kuma irin salon da ake amfani da shi wajen koyarwa. Bugu da kari kuma, ya kamata masana ilimi su yi amfani da irin ci gaban da fasaha ta kawo a wannan fanni na koyarwa.

Wasu Abubuwa Da Suka Shafi Ilimi A Duniya 

Kashi 88 na yara mata da kuma kashi 91 na yara maza, suna da ilimin Firamare, sai dai kuma mata da dama na samun ilimi mai zurfi fiye da maza, (World Economic Forum, 2019). 

A shekarar 2020, yawancin wadanda suka kammala karatun Firamare a fadin duniya baki-daya, kashi  90.14 cikin 100 ne, (UNESCO, 2021e). 

A cikin shekarar, an samu raguwar wadanda suka kammala karatun Sakandaren da kashi 77 cikin 100, (UNESCO, 2021d).

Haka nan ma, wadanda suka yi makarantar yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, kashi 86 ne cikin 100, (UNESCO, 2021c).

Wadanda suka yi yaki da jahilci ‘yan shekara 15 da wadanda suka haura haka, sun zarce kashi 83.3 cikin 100, yayin da su kuma maza suka kasance kashi 90 cikin 100, (UNESCO, 2021a; UNESCO, 2021b).

Ilimi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ilimi
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Ilimi
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Next Post
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.