ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

by Sulaiman
12 months ago
Zamfara

Jihar Zamfara ita ce ta farko a Nijeriya da ta fara amfani da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani (ZDLF) don samar wa al’ummarta muhimman fasahohin zamani don ci gaban tattalin arziki, tsarin gudanar da aiki na zamani, da ƙirƙire-ƙirƙire.

 

A ranar Larabar da ta gabata ne aka gudanar da babban taron masu ruwa da tsaki kan tsarin ilimin fasahar zamani na Zamfara a ɗakin taro na Garba Nadama a Sakatariyar JB Yakubu da ke Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT
  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, taron masu ruwa da tsakin ya haɗa da manyan cibiyoyin gwamnatin tarayya, abokan ci gaba, ’yan majalisa, malamai, da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu domin yin nazari tare da inganta tsarin.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana tsarin a matsayin wani kwakkwaran taswirar zamani da za a sa a gaba tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an aiwatar da shi sosai.

 

Ya ci gaba da cewa, “A yau mun samu wani gagarumin ci gaba a tafiyarmu ta haɗin gwiwa a jihar Zamfara ta hanyar inganta fasahar zamani, ƙirƙire-ƙirƙire, da hanyoyin samun bayanai da fasahar sadarwa.

 

“Tsarin Ilimin Fasahar Zamani nna Zamfara wani tsari ne da zai amfani buƙatun al’umma na dogon lokaci don samar wa mutanenmu ƙarfin aiki da haɓaka ƙwarewarsu a cikin duniyar fasahar zamani.

 

“Kamar yadda muka sani, ilimin fasahar zamani yana da muhimmanci don samar da ayyukan yi da samar da ingantacciyar tsarin aiki. Ba zai yiwu mu rungume hannu mu bar jihar a baya ba a zamani ilimin fasahar zamani.

 

“Wannan tsarin yana da nufin samar da ilimi a bangaren fasahar zamani kan abubuwan da suma shafi – kwamfuta, ayyukan gwamnati, da kasuwanci. Tsarin yana dubi ga jihar da kowane ɗalibi zai ƙware sosai a fannin fasahar zamani, kowane ma’aikacin gwamnati zai samu fasahar zamani don gudanar da aikin sa, kuma manyan ‘yan kasuwa da ƙanana suna da ƙwarewar faɗaɗa kasuwancinsu. Mun fara shirin aiwatar da wannan hangen nesa.

Zamfara

“Jihar Zamfara ta haɗa gwiwa da Kamfanin Oracle domin horar da matasa 3,000 a shirin ‘Cloud 2 Computing, Artificial Intelligence, Data Science, and Database Management’. Tare da makarantar Oracle, manyan makarantunmu za su samu tallafi don yaye ɗalibai masu ƙwarewa a harkar masana’antu.

 

“An fara aiki a Cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZIIT) da ke Gusau, wannan cibiya za ta kasance cibiyar ƙwararru ta yanki, da ke ba da ilimin kwamfuta da kuma samar da ƙirƙire-ƙirƙire a cikin gida. Muna da burin ganin mun ɗinke barakar fasahar zamani da kuma sanya Zamfara a matsayin cibiyar ilimin kwamfuta a Arewacin Nijeriya.”

 

Tun da farko, a jawabinsa na maraba sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, ya bayyana ƙudirin gwamnatin jihar na ganin jihar Zamfara ta kasance kan gaba wajen kawo sauyi a bangaren fasahar zamani a Arewacin Nijeriya.

 

Da take isar da saƙon fatan alheri, Sanata Ikra Aliyu Bilbis (Sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya), Shugabar Kwamitin Fasahar Zamani da Tattalin Arziki na Majalisar Dattawa, ta yaba wa Zamfara kan yadda take kan gaba a lokacin da ci gaban ƙasa ya ta’allaka kan fasahar zamani. Sanatar ta ba da gudunmawar kwamfutoci 300 ga ZITDA don tallafa wa tsarin fasahar zamani a duk faɗin jihar.

Zamfara

A jawabinsa dangane da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani na Zamfara (ZDLF), Dokta Habib Gajam, Babban Sakatare na Hukumar Bunƙasa Fasahar Watsa Labarai ta Zamfara (ZITDA), ya bayyana tsarin a matsayin wata dabarar da ta shafi mutane da aka tsara.

 

Muhimman cibiyoyi na fasahar zamani na Gwamnatin Tarayya da aka wakilta a taron masu ruwa da tsakin sun haɗa da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC), Galaxy Backbone, Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA), Cibiyar Kuka da Tauraron Ɗan Adam, da Hukumar Kare Bayanai ta Nijeriya (NDPC).

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.