• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

Farfesa Aishatu

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bincike ya nuna cewa, mata sun fi mazaje fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu saboda irin matsaloli na damuwa da suke fuskanta a rayuwar yau da kullum.

Wata fitacciyar Likitar kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ce ta bayyana haka a tattaunawarta da manema labarai jim kadan bayan sanar da nada ta Shugabar Asibitin Masu Tabin Kwakwalwa da ke Barnawa a Kaduna.

  • Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
  • Wasu Fusatattun Matasa Sun Afka Wa Tawagar Sanata Kwankwaso A Jihar Kogi

A ranar 18 ga watan Agusta 2022 Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u (MBBS, Cert. LMIH/ FIS, PGDE, MSc, MBA, PhD, FMCPsych, FWACP, IFAPA, MNIM) a matsayin shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa da ke Barnawa, Kaduna, wanda hakan ke nuna cewa, ita ce mace ta farko a fadin Arewacin Nijeriya da ta fara rike mukamin shugabancin Asibitin masu Tabin Kwakwalwa a fadin Arewacin Nijeriya.

Duk da cewa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ta taso ce daga Arewacin Nijeriya inda mata ba su cika samun damar zurfafa karatunsu na boko ba amma ta jajirce har ta samu kammala digirinta a fannin aikin likita a Jami’ar Bayero da ke Kano Nijeriya.

Ta kuma kasance Mamba na cibiyar kwararu ta ‘National Postgraduate Medical College of Nigeria (FMCPsych)’ da ‘West African College of Physician (FWACP)’.

Labarai Masu Nasaba

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Haka kuma Farfesa Aishatu ta kammala digirinta na biyu da yabo kyakyawa daga Jami’ar Liberpool da ke Landan inda ta kware fannin ‘Forensic Psychology and Criminal Inbestigation (MSc. FP&CI)’.

Farfesa Aishatu Armiya bata tsaya a nan ba don kuwa ta yi karatu na musamma a kan harkokin shugabanci da gudanarwa a Jami’ar Washington da ke kasar Amurka ta kuma yi babbar difloma a kan koyarwa daga Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara daga nan ta zarce Jami’ar Central De Nicaraguainda inda ta yi digirinta na Dakta wato digirin digirgir.

Ta kuma samu nasarra samun digirinta na biyu a fannin kasuwanci inda ta karkata kwarewar ta a kan hanyoyin tafiyar da kiwon lafiya da tafiyar da gudanar da asibitoci, ta kuma halarci tarurukan kwarruna a kan harkokin kiwon lafiya a ciki da wajen kasar nan.

Kafin nadata shugabar asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa Kaduna, ta yi aki a matsayin babbar Likitar kula da cututtukan kwakwalwa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tafawa Balewa da ke Bauchi tana kuma jagorantar likitoci masu sa ido a gidajen yarin Jos a jihar Filato.

Aishatu ce mace ta farko daga Arewa da ta samu wannan kwarewar a bangbare kula da cututtukar kwakwalwa a Nijeriya.

Ta bayar da gudummawa a fannoni da dama wajen bunkasa lafiyar al’umma a ciki da wajen kasar nan a tattaunawar ta farko bayan nadin da aka yi mat ana shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa kaduna ta bayyana cewa, Mata Sun Fi Fuskantar Yiwuwar Kanshe Kan Su Fiye Da Maza, ga dai yadda tattaunawar ta kasance a rahoton da Wakilinmu ya fruwaito mana.

Wata shaharraiyar masanaiyar ilimin kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u ta bayar da gamsashiyar dalilai da ke bayyana abubuwan da suke sanya mata suka fi fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu fiye da maza, musamman ganin sun fi fukantar matsaloli na damuwa fiye da takwarorinsu maza.

Farfesar ta bayyana haka ne a tataunawarta da manema labarai a a Kaduna, ta kuma kara da cewa, tsananin damuwa na haifar da kisan ka, damuwar da mata suka fi fuskanta sun hada da rashin kudi da matsalolin da suka shafi rayuwar zaman aure, kamar yadda binckike na bayabaya nan ya nuna.

Daga nan Farfesar ta kuma ce, an fi samun kisan kai a gidaje, makarantu, da masu fadawa cikin ruwa, an kuma fi samun mata da aikata irin wannan nau’io na kisan kai.

Ta ce, tabin hankali na daya daga cikin abubuwan da suke haifar da kisan ka da cikin al’umma.

Ta ce, “A kwai banbanci na yawan masu kashe kansu a tsakanin mata da maza, bincike ya nuna cewa, matsalolin rashin kudi da rikice-rikicen zaman aure na daga cikin dalilin da ke jefa mata kashe kansu, amma dalilan da ke jefa masa kashe kansu ya banbanta, a kan haka in ana son kawo karshen lamarin kisan kai dole a fuskance shi ta hanyar lura da banbanci a tsakanin mata da maza, don lamarin ba daidai ba ne a tsakannin maza da mata.

“A nawa ra’ayin yakamata gwamnati ta samar da kudade masu yawa don gudanar da bincike a cikin al’umma ta haka za mu samu cikakken hujjoji na sanin yadda za a kawo karshen wannan lamarin, a kan haka lamarin kula da lafiyar kwakwalwa ga al’umma ke da matukar muhuimanci a wuraren da suka hada mamakarantu gidaje da sauransu, ta haka be za a iya kamo hanyar kawo karshen yawaitar kisan kai a cikin al’umma” Farfesar ta kuma bayyana cewa, bincike ya nuna dole a fara daga gidaje ta hanyar amfani da iyaye da makwabta sannan a wuto makarantu don samar da hanyar kawo karshen wannan matsalar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariAsibitFarfesa AishatuKashe KaiMataMazaTattaunawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin Ranar Hausa Ya Gudana A Nijeriya Da Wasu Kasashen Duniya

Next Post

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

Related

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

14 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

15 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

15 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

17 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

18 hours ago
Next Post
Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.