ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

by Bello Hamza
4 years ago
Farfesa Aishatu

Farfesa Aishatu

Bincike ya nuna cewa, mata sun fi mazaje fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu saboda irin matsaloli na damuwa da suke fuskanta a rayuwar yau da kullum.

Wata fitacciyar Likitar kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ce ta bayyana haka a tattaunawarta da manema labarai jim kadan bayan sanar da nada ta Shugabar Asibitin Masu Tabin Kwakwalwa da ke Barnawa a Kaduna.

  • Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
  • Wasu Fusatattun Matasa Sun Afka Wa Tawagar Sanata Kwankwaso A Jihar Kogi

A ranar 18 ga watan Agusta 2022 Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u (MBBS, Cert. LMIH/ FIS, PGDE, MSc, MBA, PhD, FMCPsych, FWACP, IFAPA, MNIM) a matsayin shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa da ke Barnawa, Kaduna, wanda hakan ke nuna cewa, ita ce mace ta farko a fadin Arewacin Nijeriya da ta fara rike mukamin shugabancin Asibitin masu Tabin Kwakwalwa a fadin Arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ta taso ce daga Arewacin Nijeriya inda mata ba su cika samun damar zurfafa karatunsu na boko ba amma ta jajirce har ta samu kammala digirinta a fannin aikin likita a Jami’ar Bayero da ke Kano Nijeriya.

Ta kuma kasance Mamba na cibiyar kwararu ta ‘National Postgraduate Medical College of Nigeria (FMCPsych)’ da ‘West African College of Physician (FWACP)’.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Haka kuma Farfesa Aishatu ta kammala digirinta na biyu da yabo kyakyawa daga Jami’ar Liberpool da ke Landan inda ta kware fannin ‘Forensic Psychology and Criminal Inbestigation (MSc. FP&CI)’.

Farfesa Aishatu Armiya bata tsaya a nan ba don kuwa ta yi karatu na musamma a kan harkokin shugabanci da gudanarwa a Jami’ar Washington da ke kasar Amurka ta kuma yi babbar difloma a kan koyarwa daga Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara daga nan ta zarce Jami’ar Central De Nicaraguainda inda ta yi digirinta na Dakta wato digirin digirgir.

Ta kuma samu nasarra samun digirinta na biyu a fannin kasuwanci inda ta karkata kwarewar ta a kan hanyoyin tafiyar da kiwon lafiya da tafiyar da gudanar da asibitoci, ta kuma halarci tarurukan kwarruna a kan harkokin kiwon lafiya a ciki da wajen kasar nan.

Kafin nadata shugabar asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa Kaduna, ta yi aki a matsayin babbar Likitar kula da cututtukan kwakwalwa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tafawa Balewa da ke Bauchi tana kuma jagorantar likitoci masu sa ido a gidajen yarin Jos a jihar Filato.

Aishatu ce mace ta farko daga Arewa da ta samu wannan kwarewar a bangbare kula da cututtukar kwakwalwa a Nijeriya.

Ta bayar da gudummawa a fannoni da dama wajen bunkasa lafiyar al’umma a ciki da wajen kasar nan a tattaunawar ta farko bayan nadin da aka yi mat ana shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa kaduna ta bayyana cewa, Mata Sun Fi Fuskantar Yiwuwar Kanshe Kan Su Fiye Da Maza, ga dai yadda tattaunawar ta kasance a rahoton da Wakilinmu ya fruwaito mana.

Wata shaharraiyar masanaiyar ilimin kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u ta bayar da gamsashiyar dalilai da ke bayyana abubuwan da suke sanya mata suka fi fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu fiye da maza, musamman ganin sun fi fukantar matsaloli na damuwa fiye da takwarorinsu maza.

Farfesar ta bayyana haka ne a tataunawarta da manema labarai a a Kaduna, ta kuma kara da cewa, tsananin damuwa na haifar da kisan ka, damuwar da mata suka fi fuskanta sun hada da rashin kudi da matsalolin da suka shafi rayuwar zaman aure, kamar yadda binckike na bayabaya nan ya nuna.

Daga nan Farfesar ta kuma ce, an fi samun kisan kai a gidaje, makarantu, da masu fadawa cikin ruwa, an kuma fi samun mata da aikata irin wannan nau’io na kisan kai.

Ta ce, tabin hankali na daya daga cikin abubuwan da suke haifar da kisan ka da cikin al’umma.

Ta ce, “A kwai banbanci na yawan masu kashe kansu a tsakanin mata da maza, bincike ya nuna cewa, matsalolin rashin kudi da rikice-rikicen zaman aure na daga cikin dalilin da ke jefa mata kashe kansu, amma dalilan da ke jefa masa kashe kansu ya banbanta, a kan haka in ana son kawo karshen lamarin kisan kai dole a fuskance shi ta hanyar lura da banbanci a tsakanin mata da maza, don lamarin ba daidai ba ne a tsakannin maza da mata.

“A nawa ra’ayin yakamata gwamnati ta samar da kudade masu yawa don gudanar da bincike a cikin al’umma ta haka za mu samu cikakken hujjoji na sanin yadda za a kawo karshen wannan lamarin, a kan haka lamarin kula da lafiyar kwakwalwa ga al’umma ke da matukar muhuimanci a wuraren da suka hada mamakarantu gidaje da sauransu, ta haka be za a iya kamo hanyar kawo karshen yawaitar kisan kai a cikin al’umma” Farfesar ta kuma bayyana cewa, bincike ya nuna dole a fara daga gidaje ta hanyar amfani da iyaye da makwabta sannan a wuto makarantu don samar da hanyar kawo karshen wannan matsalar.

Kashe Kansu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.