ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

by Bello Hamza
4 years ago
Farfesa Aishatu

Farfesa Aishatu

Bincike ya nuna cewa, mata sun fi mazaje fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu saboda irin matsaloli na damuwa da suke fuskanta a rayuwar yau da kullum.

Wata fitacciyar Likitar kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ce ta bayyana haka a tattaunawarta da manema labarai jim kadan bayan sanar da nada ta Shugabar Asibitin Masu Tabin Kwakwalwa da ke Barnawa a Kaduna.

  • Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
  • Wasu Fusatattun Matasa Sun Afka Wa Tawagar Sanata Kwankwaso A Jihar Kogi

A ranar 18 ga watan Agusta 2022 Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u (MBBS, Cert. LMIH/ FIS, PGDE, MSc, MBA, PhD, FMCPsych, FWACP, IFAPA, MNIM) a matsayin shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa da ke Barnawa, Kaduna, wanda hakan ke nuna cewa, ita ce mace ta farko a fadin Arewacin Nijeriya da ta fara rike mukamin shugabancin Asibitin masu Tabin Kwakwalwa a fadin Arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ta taso ce daga Arewacin Nijeriya inda mata ba su cika samun damar zurfafa karatunsu na boko ba amma ta jajirce har ta samu kammala digirinta a fannin aikin likita a Jami’ar Bayero da ke Kano Nijeriya.

Ta kuma kasance Mamba na cibiyar kwararu ta ‘National Postgraduate Medical College of Nigeria (FMCPsych)’ da ‘West African College of Physician (FWACP)’.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Haka kuma Farfesa Aishatu ta kammala digirinta na biyu da yabo kyakyawa daga Jami’ar Liberpool da ke Landan inda ta kware fannin ‘Forensic Psychology and Criminal Inbestigation (MSc. FP&CI)’.

Farfesa Aishatu Armiya bata tsaya a nan ba don kuwa ta yi karatu na musamma a kan harkokin shugabanci da gudanarwa a Jami’ar Washington da ke kasar Amurka ta kuma yi babbar difloma a kan koyarwa daga Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara daga nan ta zarce Jami’ar Central De Nicaraguainda inda ta yi digirinta na Dakta wato digirin digirgir.

Ta kuma samu nasarra samun digirinta na biyu a fannin kasuwanci inda ta karkata kwarewar ta a kan hanyoyin tafiyar da kiwon lafiya da tafiyar da gudanar da asibitoci, ta kuma halarci tarurukan kwarruna a kan harkokin kiwon lafiya a ciki da wajen kasar nan.

Kafin nadata shugabar asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa Kaduna, ta yi aki a matsayin babbar Likitar kula da cututtukan kwakwalwa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tafawa Balewa da ke Bauchi tana kuma jagorantar likitoci masu sa ido a gidajen yarin Jos a jihar Filato.

Aishatu ce mace ta farko daga Arewa da ta samu wannan kwarewar a bangbare kula da cututtukar kwakwalwa a Nijeriya.

Ta bayar da gudummawa a fannoni da dama wajen bunkasa lafiyar al’umma a ciki da wajen kasar nan a tattaunawar ta farko bayan nadin da aka yi mat ana shugabar Asibitin Masu Cutar Kwakwalwa na Barnawa kaduna ta bayyana cewa, Mata Sun Fi Fuskantar Yiwuwar Kanshe Kan Su Fiye Da Maza, ga dai yadda tattaunawar ta kasance a rahoton da Wakilinmu ya fruwaito mana.

Wata shaharraiyar masanaiyar ilimin kwakwalwa, Farfesa Aishatu Yusha’u ta bayar da gamsashiyar dalilai da ke bayyana abubuwan da suke sanya mata suka fi fuskantar barazanar yiwuwar kashe kansu fiye da maza, musamman ganin sun fi fukantar matsaloli na damuwa fiye da takwarorinsu maza.

Farfesar ta bayyana haka ne a tataunawarta da manema labarai a a Kaduna, ta kuma kara da cewa, tsananin damuwa na haifar da kisan ka, damuwar da mata suka fi fuskanta sun hada da rashin kudi da matsalolin da suka shafi rayuwar zaman aure, kamar yadda binckike na bayabaya nan ya nuna.

Daga nan Farfesar ta kuma ce, an fi samun kisan kai a gidaje, makarantu, da masu fadawa cikin ruwa, an kuma fi samun mata da aikata irin wannan nau’io na kisan kai.

Ta ce, tabin hankali na daya daga cikin abubuwan da suke haifar da kisan ka da cikin al’umma.

Ta ce, “A kwai banbanci na yawan masu kashe kansu a tsakanin mata da maza, bincike ya nuna cewa, matsalolin rashin kudi da rikice-rikicen zaman aure na daga cikin dalilin da ke jefa mata kashe kansu, amma dalilan da ke jefa masa kashe kansu ya banbanta, a kan haka in ana son kawo karshen lamarin kisan kai dole a fuskance shi ta hanyar lura da banbanci a tsakanin mata da maza, don lamarin ba daidai ba ne a tsakannin maza da mata.

“A nawa ra’ayin yakamata gwamnati ta samar da kudade masu yawa don gudanar da bincike a cikin al’umma ta haka za mu samu cikakken hujjoji na sanin yadda za a kawo karshen wannan lamarin, a kan haka lamarin kula da lafiyar kwakwalwa ga al’umma ke da matukar muhuimanci a wuraren da suka hada mamakarantu gidaje da sauransu, ta haka be za a iya kamo hanyar kawo karshen yawaitar kisan kai a cikin al’umma” Farfesar ta kuma bayyana cewa, bincike ya nuna dole a fara daga gidaje ta hanyar amfani da iyaye da makwabta sannan a wuto makarantu don samar da hanyar kawo karshen wannan matsalar.

Kashe Kansu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.