• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Dage Mukabala Da Dakta Idris Bisa Kalamansa A Kan Manzon Allah – Hukumar Shari’a

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Muka Dage Mukabala Da Dakta Idris Bisa Kalamansa A Kan Manzon Allah – Hukumar Shari’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi ta dage zaman tattaunawa da ta shirya a tsakaninta da malamai da kuma Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bisa wani furuci da ya yi na cewa ‘Ko taimakon Manzon Allah ma ba su so’ furucin da ya janyo zafafan muhawara a cikin garin ta Bauchi da ke waye da ake ganin kamar malamai bai yi amfani da lafuza masu kyau ba ga Manzon Allah.

Ita dai hukumar Shari’a ta zargi Malam Idris da yin amfani da kalmar da ya kasance na kasanci ga Manzon da munanawa tare da rashin ladabi, don haka ne ta shirya zama da shi domin ankarar da shi wannan kuskuren.

  • Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Idan za a tuna dai hukumar ta ware yau Asabar 8 ga watan Afrilu domin yin wannan zaman amma daga bisani aka ga ta dage zuwa wani lokacin da ba a sanar ba zuwa yanzu.

Malam Mustapha Baba Ilaleh, shugaban hukumar shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi ya shaida ta cikin hirarsa da wata gidan rediyo cewa, nan ba da jimawa ba za su sake sanar da sabon ranar da za a yi wannan zaman.

Ya ke cewa: “Lallai mun shirya za a yi zama da Malam Idris Abdul’aziz dangane da wasu kalmomi da ya fada; to kalmar karshe da ya furta sai ya zama ya yi wa al’ummar musulmai zafi musamman wadanda suka kasance masoyan Manzon Allah (SAW). To wannan kalmar ya daga hankali sosai a ciki da wajen gari. Hakan ya sa aka kira zama na musamman da shi aka kuma tanadi malamai domin a zo a zauna a tattauna da shi a ankarar da shi munanan kalma da ya ambata ko dai a yarda da muninsu don babu maganar kariya a wannan kalmar domin kalmomi ne wadanda da wuya su dauki wani tawili.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

“Wannan ya sanya muka yi shirye-shirye domin a yi a ranar Asabar 8 ga watan Afrilu amma sakamakon wasu abubuwa da muka ga ya dace mu kammala su mu tanadasu ya sa muka ga ya dace mu daga daga baya za a yi wannan zaman.”

“Shi wannan zaman mun shirya shi ne sakamakon wata ibara wato wata jimla da shi Malam Idris ya fada lokacin da yake kokarin kore istigasa da istina neman taimako ko neman agaji ba a yi a wajen kowa sai Allah (SWT), ya ce, baya nema a wajen Inyasi, ba ya nemi a wajen Tijjani ba ya nema a wajen Abdulkadiri ba ya nema a wajen Shehu Danfodio sai ya ce kai ko (Wa’izabilla) ko Manzon Allah ma ba mu neman taimako a wajensa, ‘ko Manzon Allah ma ba mu bukatar taimakonsa’, wa’iyazubillah.

“To ka ga wannan wata jimlace da ba za ta dauki wani tawili ba. Malamai suke fassara wannan jimlar da cewa akwai ihana ga Annabi (SAW) wato akwai kaskantawa ga Annabi (SAW) kuma akwai abun da ake kira ‘su’ul’adabi’ wadannan suka sabbaba muka ga ya kamata a nemeshi ya zo ya yi bayani tattare da wannan jimlar tasa ta karshe don mu a kanta muke magana. Da kuma munanta ladabi wadanda bai kamata ya fadi wadannan kalmomin ba.”

Malam Mustapha Ilaleh ya karyata batun da ke cewa sun dage zaman ne sakamakon janyewa da kungiyar Izalah ta yi a wajen zaman, ya ce sam ba wannan ne dalilin da ya janyo dage zaman ba domin tun kafin kungiyar ta aiko da wasikarta sun riga ma sun cimma matsayar dage zaman.

Ya ce, makasudin shirya zaman shi ne domin a tabbatar da yin gaskiya da fito da batutuwa daga littafai na magabata.

Daga nan Baba Ilaleh ya yi kira ga al’umma da a kowani lokaci suke amsar tacaccen ilimi sannan jama’a su kara sanin hakkokin Manzon Allah (SAW) don a so shi so ta gaskiya ta hakika a bi shi bi ta sunnar gaske ba ta riyawa a baki ba kawai.

A cewarsa, akwai bukatar a kullum a ke amfani da hujja mai karfi da hujja mai asali tare da bin fassara da ma’anoni kamar yadda magabata suka bayar a sullisi na Kur’ani ko hadisai.

Daga nan ya jawo hankalin jama’a da cewa koda irin wannan abun ya faru kada su dauki doka a hannunsu kuma kada su furta kalamai marasa kan gado domin ya bada tabbacin cewa za su bi lamarin kuma za a fito da hakikanin abubuwan da suka dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Next Post

An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

9 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

12 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

12 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

14 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

14 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

15 hours ago
Next Post
An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.