• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Dage Mukabala Da Dakta Idris Bisa Kalamansa A Kan Manzon Allah – Hukumar Shari’a

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Muka Dage Mukabala Da Dakta Idris Bisa Kalamansa A Kan Manzon Allah – Hukumar Shari’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi ta dage zaman tattaunawa da ta shirya a tsakaninta da malamai da kuma Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bisa wani furuci da ya yi na cewa ‘Ko taimakon Manzon Allah ma ba su so’ furucin da ya janyo zafafan muhawara a cikin garin ta Bauchi da ke waye da ake ganin kamar malamai bai yi amfani da lafuza masu kyau ba ga Manzon Allah.

Ita dai hukumar Shari’a ta zargi Malam Idris da yin amfani da kalmar da ya kasance na kasanci ga Manzon da munanawa tare da rashin ladabi, don haka ne ta shirya zama da shi domin ankarar da shi wannan kuskuren.

  • Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Idan za a tuna dai hukumar ta ware yau Asabar 8 ga watan Afrilu domin yin wannan zaman amma daga bisani aka ga ta dage zuwa wani lokacin da ba a sanar ba zuwa yanzu.

Malam Mustapha Baba Ilaleh, shugaban hukumar shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi ya shaida ta cikin hirarsa da wata gidan rediyo cewa, nan ba da jimawa ba za su sake sanar da sabon ranar da za a yi wannan zaman.

Ya ke cewa: “Lallai mun shirya za a yi zama da Malam Idris Abdul’aziz dangane da wasu kalmomi da ya fada; to kalmar karshe da ya furta sai ya zama ya yi wa al’ummar musulmai zafi musamman wadanda suka kasance masoyan Manzon Allah (SAW). To wannan kalmar ya daga hankali sosai a ciki da wajen gari. Hakan ya sa aka kira zama na musamman da shi aka kuma tanadi malamai domin a zo a zauna a tattauna da shi a ankarar da shi munanan kalma da ya ambata ko dai a yarda da muninsu don babu maganar kariya a wannan kalmar domin kalmomi ne wadanda da wuya su dauki wani tawili.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

“Wannan ya sanya muka yi shirye-shirye domin a yi a ranar Asabar 8 ga watan Afrilu amma sakamakon wasu abubuwa da muka ga ya dace mu kammala su mu tanadasu ya sa muka ga ya dace mu daga daga baya za a yi wannan zaman.”

“Shi wannan zaman mun shirya shi ne sakamakon wata ibara wato wata jimla da shi Malam Idris ya fada lokacin da yake kokarin kore istigasa da istina neman taimako ko neman agaji ba a yi a wajen kowa sai Allah (SWT), ya ce, baya nema a wajen Inyasi, ba ya nemi a wajen Tijjani ba ya nema a wajen Abdulkadiri ba ya nema a wajen Shehu Danfodio sai ya ce kai ko (Wa’izabilla) ko Manzon Allah ma ba mu neman taimako a wajensa, ‘ko Manzon Allah ma ba mu bukatar taimakonsa’, wa’iyazubillah.

“To ka ga wannan wata jimlace da ba za ta dauki wani tawili ba. Malamai suke fassara wannan jimlar da cewa akwai ihana ga Annabi (SAW) wato akwai kaskantawa ga Annabi (SAW) kuma akwai abun da ake kira ‘su’ul’adabi’ wadannan suka sabbaba muka ga ya kamata a nemeshi ya zo ya yi bayani tattare da wannan jimlar tasa ta karshe don mu a kanta muke magana. Da kuma munanta ladabi wadanda bai kamata ya fadi wadannan kalmomin ba.”

Malam Mustapha Ilaleh ya karyata batun da ke cewa sun dage zaman ne sakamakon janyewa da kungiyar Izalah ta yi a wajen zaman, ya ce sam ba wannan ne dalilin da ya janyo dage zaman ba domin tun kafin kungiyar ta aiko da wasikarta sun riga ma sun cimma matsayar dage zaman.

Ya ce, makasudin shirya zaman shi ne domin a tabbatar da yin gaskiya da fito da batutuwa daga littafai na magabata.

Daga nan Baba Ilaleh ya yi kira ga al’umma da a kowani lokaci suke amsar tacaccen ilimi sannan jama’a su kara sanin hakkokin Manzon Allah (SAW) don a so shi so ta gaskiya ta hakika a bi shi bi ta sunnar gaske ba ta riyawa a baki ba kawai.

A cewarsa, akwai bukatar a kullum a ke amfani da hujja mai karfi da hujja mai asali tare da bin fassara da ma’anoni kamar yadda magabata suka bayar a sullisi na Kur’ani ko hadisai.

Daga nan ya jawo hankalin jama’a da cewa koda irin wannan abun ya faru kada su dauki doka a hannunsu kuma kada su furta kalamai marasa kan gado domin ya bada tabbacin cewa za su bi lamarin kuma za a fito da hakikanin abubuwan da suka dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Next Post

An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

3 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

6 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

6 hours ago
Mukabala
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

8 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

9 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

10 hours ago
Next Post
An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

An Kori Masu Koyarwa 12 Kawo Yanzu A Premier Ta Ingila

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Mukabala

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.