• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas

by yahuzajere
3 years ago
in Siyasa
0
Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Matasan Arewa Mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya bayyana cewa sun gamsu da manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bisa yadda suka ƙunshi dabarun magance manyan matsalolin da suka addabi Nijeriya a zamanin nan.

A cewar Galadanci, lokaci ya yi da ‘Yan Nijeriya za su zabura su tabbatar da nagarta wajen zaɓen shugabannin da suka fi cancanta a zaɓen 2023 domin fita daga halin da suke ciki na rashin tsaro da tsadar rayuwa.

  • Shugaba Buhari Ya Gana Da Sarki Charles III Na Birtaniya A Landon

Ya ƙara da cewa, “Ƙungiyarmu ta Gamayyar Matasan Arewa a Legas, mun fahimci manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Dr Rabi’u Musa Kwankwaso kuma mun gamsu da jawabinsa da ya yi wa al’ummar Nijeriya da ma duniya baki ɗaya. Abin da ya fi ɗaukar hankalinmu a jawabin nasa shi ne idan Allah ya ba su ikon cin nasara a zaɓen 2023, ya ƙudiri aniyar magance matsalolin tsaron cikin gida a Nijeriya da iyyakokinta, musamman ƙudirin da ya yi na zai ɗauki sojoji kimanin miliyan ɗaya da ‘yansanda miliyan ɗaya da sauran jami’an tsaro waɗanda za a tantance su tun daga matakin ƙaramar hukumarsu har zuwa jiha, yin hakan babbar nasara ce ga ƙasarmu da kuma ‘yan ƙasa baki ɗaya. Sannan da batun bunƙasa harkar ilimi da sauran tsare-tsare na alheri wanda waɗannan maganganu su ne suka ba mu damar mu taya su da addu’o’inmu na alheri a kan Allah ya cika musu burinsu mu samu zaman lafiya da ci gaban al’umma.

“Ƙasarmu mun san yadda Allah ya yi mata arzikin ma’adanai masu daraja waɗanda muna ji muna gani wasu na yi mana kisan gillah, suna amfani da wannan damar suna kwasar dukiyar. Sun haɗa baki da baƙin haure an hana mu zaman lafiya. Don haka wannan lokaci ne da za mu mu fito domin ganin an daina yi wa al’ummar Nijeriya wasan wawaso da dukiyar da Allah ya bayar ga ƙasar domin al’ummar Nijeriya su amfana. Ba kuɗi za a ba mu ba domin muna dimokraɗiyya ne a yanzu, ya kamata mu tashi tsaye mu kawo wa ƙasarmu ci gaban da za mu yi alfari da ita a matsayin Nijeriya ƙasa ɗaya mai al’umma ɗaya da ke samun bunƙasa.

“Muna kira ga ‘Yan Nijeriya a kan su fahimci cewa abin da muka fi buƙata a wannan zaɓen na 2023 da za a yi shi ne mu yi watsi da harkar ubangida, kowane ubangida yana da wani muradin kansa a fagen siyasa kuma wannan muradin ba don kishin ci gaban jama’a ba ne sai dai ci gaban kansa da iyalansa. Don haka wannan ne lokaci mafi dacewa da za mu yaƙi azzalimai waɗanda ana yi mana kisan gillah ba dare ba rana amma ba su damu ba, yadda za su ci gaba da mulki da ɗora nasu a kai kawai suke ƙoƙarin yi saboda sun mayar da mulkin ƙasar ya zama na gado.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Ya ƙara da cewa, yadda aka riƙa sayen wakilai masu zaɓe tun daga zaɓen fitar da gwani, manuniya ce ta neman ƙara danne talakan Nijeriya.

“A idon duniya manyan ‘yan takara suka dinga sayen wakilai masu zaɓe da ake ce wa ‘delegate’ domin su ci gaba da kassara mu. Talakan Nijeriya ya san irin uƙubar da yake ciki. Don haka muna ƙara yin kira ga shugabannin manyan ƙasashe na duniya, matuƙar suna son ɗorewar dimokuraɗiyya a Nijeriya, su taimaka wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zaɓi waɗanda suka cancanta da za su fitar da su daga halin da ƙasar take ciki. Duk wani ɗan ƙasa nagari da ka sani ya gaji da kisan gilla da tsadar rayuwa. Mu a matsayinmu na gamayyar matasan arewa da ke Legas, muna kira ga dukkan ‘yan ƙasa ba tare da bambancin ƙabila ko addini ba, mu tashi tsaye mu zaɓi cancanta, wannan ne kaɗai zai kai mu ga tudun mun tsira a 2023.” Ya bayyana.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ASUU: Ndume Ya Bukaci A Zabtare Albashin ‘Yan Majalisa Kashi 50 Cikin 100 A Biya Malaman Jami’a

Next Post

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

5 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

6 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
A Shirye Kwankwaso Yake Ya Karbi Alasan Ado Doguwa A Kwankwasiyya —Rurum

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.