• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Naɗa Mataimakin Dr. Ahmed Gumi A Masallacin Sultan Bello – JNI

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Muka Naɗa Mataimakin Dr. Ahmed Gumi A Masallacin Sultan Bello – JNI
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta ƙasa ta bayyana cewa Masallacin Sultan Bello da ke Unguwar Sarki, Kaduna ba na zuriyar Marigayi Shaikh Abubakar Gumi ko na wani mutum ba ne, na al’ummar Musulmi ne gaba ɗaya, wanda ke ƙarƙashin kulawarta.

Ta kuma ce, naɗin mataimakin mai gabatar da Tafsiri a masallacin da aka yi, an yi shi ne bisa ƙa’ida, ba wai an yi ne don a muzguna wa wasu ko wani mutum ba.

  • Sheikh Gumi Ga Tinubu: Ka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga, Kada Ka Zama Irin Buhari
  • Hukuncin Zaben Adamawa: Na Rungumi Kaddara – Binani

JNI ta ce, Limamai, mataimakansu, masu wa’azi da mataimakansu, da duk masu kula da harkar masallacin, duk suna ƙarƙashin kulawarta ne, na abin da ya shafi albashi da sauran hidindimun masallacin.

Sakataren gudanarwa na ƙungiyar JNI, Malam Yusuf Bida ne ya bayyana haka a ranar Litinin a ofishin ƙungiyar da ke Kaduna a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai dangane da wani rubutu da aka yi a shafukan sada zumunta kan naɗin wanda zai zama mataimaki ga Dr Ahmad Gumi wurin gabatar da Tafsiri.

Rubutun wanda ɗaya daga cikin ɗaliban Shaikh Dr. Ahmad Gumi ya yi, ya yi iƙirarin cewa sabon mataimakin mai gabatar da Tafsiri a masallacin, ba mabiyi ne ga makarantar Marigayi Sheikh Abubakar Gumi ba.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

A rubutun, an kuma bayyana cewa, wasu mutane ne da ba su da alaƙa da masallacin da koyarwar Marigayi Sheikh Abubakar Gumi suka yi naɗin mataimakin, don haka ba za su amince da shi ba.

Haka kuma, a cikin rubutun na ɗalibin Dr Gumin, sun jawo hankalin mabiyansu a duk faɗin ƙasar nan da su yi watsi da wannan naɗi na mataimaki da aka yi wa Gumin, inda suka yi zargin cewa, ba a taɓa naɗa wani mataimaki ba, kafin hawan Dr. Gumi kan kujerar.

Don haka, sai ƙungiyar ta Jama’atu ta ce, Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ne da kansa ya sanya hannu a takardar naɗin Dr. Muhammad Jamil Salis a matsayin mataimakin mai tafsiri a wannan masallaci.

“Muna so mu yi cikakken bayani game da naɗa mai Tafsiri a masallacin Sultan Bello. Lokacin da Allah ya yi wa Sheikh Abubakar Gumi rasuwa, Marigayi Sheikh Halliru Binji daga Sakkwato ne aka naɗa domin ci gaba da gudanar da Tafsiri, a ranar 25 ga watan Janairun 1993,  har ya amince, amma kafin Azumi ya zagayo, sai Allah ya yi masa rasuwa.

“Bayan rasuwar Farfesa Halliru Binji ne sai aka naɗa Marigayi Sheikh Lawal Abubakar, inda ya kwashe shekaru yana gudanar da Tafsirin, bayan rasuwarsa sai aka naɗa Limamin masallacin Kwalejin Rimi da ke Kaduna, Marigayi Sheikh Umar Hasan.

Bayan ya kwashe kimanin shekaru biyu yana gabatar da Tafsirin, sai aka yi shawarar sanya abin cikin tsari, inda aka naɗa Sheikh Dr. Ahmad Gumi a matsayin wanda zai gudanar da Tafsirin, sakamakon rahoton wani kwamitin da Kanar Hamid Ali ya jagoranta,” in ji Jama’atu.

Don haka, sai Bida ya tabbatar wa duniya cewa, har yana rantsuwa, ba an yi wannan naɗi na mataimakin mai Tafsirin ba ne da wata mummunar manufa, an yi ne don Allah, don ɗaukakar musulunci.

A cewar Malam Bida, an yi wancan rubutun ne da nufin tunzura jama’a da haifar da hargitsi a cikin masallacin da aka daɗe ana samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Don haka sai Malam Yusuf Bida ya yi ƙarin haske da cewa naɗin Limamai da mataimakansu a masallacin Sultan Bello, haƙƙi ne na Jama’atu, wanda ta daɗe tana yi shekara da shekaru.

Ya ƙara da cewa, bayan an gudanar gwaji na ilimi da sauran fannoni, sai aka cimma matsaya na naɗa wanda ya fi kowa cancanta a matsayin Limami ko mataimakinsa ko mai gabatar da Tafsiri a masallacin. “Da haka ne aka naɗa Shaikh Dr Ahmed Gumi, wanda a yanzu shi ne ke gabatar Tafsiri a masallacin.

Bida ya kuma yi kira ga jami’an tsaro a jihar da hukumar kula da masallacin da su gaggauta ɗaukar ƙwararan matakai a kan duk wani abu da ke ƙoƙarin haifar da rikici a masallacin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Angola Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Next Post

Kasa Da Kasa Na Begen Ci Gaban Kasar Sin Mai Inganci Za Ta Kara Kawo Dama Ga Duniya

Related

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

4 minutes ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

1 hour ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

4 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

13 hours ago
Next Post
Sin

Kasa Da Kasa Na Begen Ci Gaban Kasar Sin Mai Inganci Za Ta Kara Kawo Dama Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.