• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi

by Abubakar Abba
9 months ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗaruruwan masu sharar manyan tititunan Jihar Kaduna, wanda akasarinsu mata ne da gwamnatin jihar ta ɗauka aiki sun gudanar da zanga-zangar lumana.

Sun yi zanga-zangar ce a kan gazawar gwamntin jihar na biyansu albashinsu na tsawon watanni biyar da kuma batun korar bazata da aka yi masu.

  • Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Fiye Da 200 A Kaduna – SEMA

Zanga-zangar ta gudana ne a ranar Litinin a wajen ƙofar hukumar raya birane mallakar gwamnatin Jihar Kaduna (KCTA), da ke a kan titin Ahmadu Bello.

Sun yi zaman dirshan na wajen awa uku kan titin na Ahmadu Bello, inda hakan ya haifar da dakatar da zirga-zirgar ababen hawa wanda sai da Ƴansanda suka roƙe su, kafin suka bar kan titin.

Ɗaya daga cikin mai kulawa da masu yin sharar a titin Ali Akilu, Fatima Inusa ta shaida wa wakilinmu cewa, “Muna tsaka da aikin ba tare da umarni daga mahukuntan hukumar na cewa an dakatar da mu ba, sai muka ga an kawo wasu sabbin masu yin sharar, inda har aka fara dambe a tsakanin ɗaya daga cikin tsaffin masu yin sharar da wata sabuwar mai shara kan ta ga tana share titin da aka ware mata don ta rinƙa sharewa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

“Na buƙaci jin ba’asi, sai sabuwar shugabar mai kulawa da sabbin masu sharar ta ce min ai mu an dakatar da mu daga yin aiki, su ne yanzu aka ɗauka don su rinƙa yin aikin”.

“Bayan an kwana biyu, sai aka turo mana sakon karta kwana a wayoyinmu cewa wai an dakatar damu. A yanzu haka akasarinmu bashi ya yi mana katutu, wasun mu ma ba su da abincin da za su ciyar da iyalansu saboda ƙin biyanmu albashinmu.”

Ita ma wata mai aikin, Farida Nuhu ta ce, “A kullum da ƙarfe hudu na dare muke barin gidajenmu don zuwa yin aikin in ban da ranar Lahadi da hukumar ta ware a matsayin ranar hutunmu, kuma muna yin aikin ne a cikin hatsari, domin a yanzu haka akwai yaron da mota ta kaɗe shi yana kan aiki, dole muke fita da wuri kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna”.

Shi ma wani mai aikin, Idris Ashiru ya ce, ” Muna fitowa zuwa gun aikin da duku-duku ne, kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna, domin akwai wata mata mai aikin da mota ta kaɗe ta a babban titin Kawo har ta mutu, sannan akwai kuma wata a Kabala da mota ta taka ta, amma ba ta mutu ba, sai kuma wani mai aikin da mota ta kaɗe shi wanda a yanzu yana asibitin kwarraun na Shika an kwantar da shi. Komai ruwan sama ko sanyi, haka muke fitowa zuwa gun aikin, mu buƙatarmu ga gwamnatin shi ne, ta biya mu albashinmu kawai.”

Wakilinmu ya tuntubi shugaban masu kula da tsaftace muhalli da ke aiki a karkashin hukumar ta KCTA, Dakta Umar Lurwanu kan batun, inda ya ce, ba su da wata masaniya kan ɗaukar wasu sabbin masu aikin da kuma batun korar tsoffin masu yin aikin, amma maganar daga sama take, sannan suna yin dukkan mai yuwa don ganin an biya kowa hakkinsa.

Ya ce, “Ba mu san komai a kan yadda aka tsara ɗaukar sabbin ma’aikatan da kuma korar tsaffin ma’aikatan ba, mun gansu kawai son zo ƙofar hukumar suna zanga-zanga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaSharaTsafta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kazancewar Matsalar Tsaro A Kwanan Nan…

Next Post

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Related

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

21 minutes ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

1 hour ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

2 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

4 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

8 hours ago
Next Post
Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.