• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi

by Abubakar Abba
11 months ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗaruruwan masu sharar manyan tititunan Jihar Kaduna, wanda akasarinsu mata ne da gwamnatin jihar ta ɗauka aiki sun gudanar da zanga-zangar lumana.

Sun yi zanga-zangar ce a kan gazawar gwamntin jihar na biyansu albashinsu na tsawon watanni biyar da kuma batun korar bazata da aka yi masu.

  • Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Fiye Da 200 A Kaduna – SEMA

Zanga-zangar ta gudana ne a ranar Litinin a wajen ƙofar hukumar raya birane mallakar gwamnatin Jihar Kaduna (KCTA), da ke a kan titin Ahmadu Bello.

Sun yi zaman dirshan na wajen awa uku kan titin na Ahmadu Bello, inda hakan ya haifar da dakatar da zirga-zirgar ababen hawa wanda sai da Ƴansanda suka roƙe su, kafin suka bar kan titin.

Ɗaya daga cikin mai kulawa da masu yin sharar a titin Ali Akilu, Fatima Inusa ta shaida wa wakilinmu cewa, “Muna tsaka da aikin ba tare da umarni daga mahukuntan hukumar na cewa an dakatar da mu ba, sai muka ga an kawo wasu sabbin masu yin sharar, inda har aka fara dambe a tsakanin ɗaya daga cikin tsaffin masu yin sharar da wata sabuwar mai shara kan ta ga tana share titin da aka ware mata don ta rinƙa sharewa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

“Na buƙaci jin ba’asi, sai sabuwar shugabar mai kulawa da sabbin masu sharar ta ce min ai mu an dakatar da mu daga yin aiki, su ne yanzu aka ɗauka don su rinƙa yin aikin”.

“Bayan an kwana biyu, sai aka turo mana sakon karta kwana a wayoyinmu cewa wai an dakatar damu. A yanzu haka akasarinmu bashi ya yi mana katutu, wasun mu ma ba su da abincin da za su ciyar da iyalansu saboda ƙin biyanmu albashinmu.”

Ita ma wata mai aikin, Farida Nuhu ta ce, “A kullum da ƙarfe hudu na dare muke barin gidajenmu don zuwa yin aikin in ban da ranar Lahadi da hukumar ta ware a matsayin ranar hutunmu, kuma muna yin aikin ne a cikin hatsari, domin a yanzu haka akwai yaron da mota ta kaɗe shi yana kan aiki, dole muke fita da wuri kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna”.

Shi ma wani mai aikin, Idris Ashiru ya ce, ” Muna fitowa zuwa gun aikin da duku-duku ne, kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna, domin akwai wata mata mai aikin da mota ta kaɗe ta a babban titin Kawo har ta mutu, sannan akwai kuma wata a Kabala da mota ta taka ta, amma ba ta mutu ba, sai kuma wani mai aikin da mota ta kaɗe shi wanda a yanzu yana asibitin kwarraun na Shika an kwantar da shi. Komai ruwan sama ko sanyi, haka muke fitowa zuwa gun aikin, mu buƙatarmu ga gwamnatin shi ne, ta biya mu albashinmu kawai.”

Wakilinmu ya tuntubi shugaban masu kula da tsaftace muhalli da ke aiki a karkashin hukumar ta KCTA, Dakta Umar Lurwanu kan batun, inda ya ce, ba su da wata masaniya kan ɗaukar wasu sabbin masu aikin da kuma batun korar tsoffin masu yin aikin, amma maganar daga sama take, sannan suna yin dukkan mai yuwa don ganin an biya kowa hakkinsa.

Ya ce, “Ba mu san komai a kan yadda aka tsara ɗaukar sabbin ma’aikatan da kuma korar tsaffin ma’aikatan ba, mun gansu kawai son zo ƙofar hukumar suna zanga-zanga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaSharaTsafta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kazancewar Matsalar Tsaro A Kwanan Nan…

Next Post

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Related

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

1 hour ago
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
Labarai

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

3 hours ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

4 hours ago
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

13 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

13 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

14 hours ago
Next Post
Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.