ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi

by Abubakar Abba
2 years ago
Kaduna

Ɗaruruwan masu sharar manyan tititunan Jihar Kaduna, wanda akasarinsu mata ne da gwamnatin jihar ta ɗauka aiki sun gudanar da zanga-zangar lumana.

Sun yi zanga-zangar ce a kan gazawar gwamntin jihar na biyansu albashinsu na tsawon watanni biyar da kuma batun korar bazata da aka yi masu.

  • Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Fiye Da 200 A Kaduna – SEMA

Zanga-zangar ta gudana ne a ranar Litinin a wajen ƙofar hukumar raya birane mallakar gwamnatin Jihar Kaduna (KCTA), da ke a kan titin Ahmadu Bello.

ADVERTISEMENT

Sun yi zaman dirshan na wajen awa uku kan titin na Ahmadu Bello, inda hakan ya haifar da dakatar da zirga-zirgar ababen hawa wanda sai da Ƴansanda suka roƙe su, kafin suka bar kan titin.

Ɗaya daga cikin mai kulawa da masu yin sharar a titin Ali Akilu, Fatima Inusa ta shaida wa wakilinmu cewa, “Muna tsaka da aikin ba tare da umarni daga mahukuntan hukumar na cewa an dakatar da mu ba, sai muka ga an kawo wasu sabbin masu yin sharar, inda har aka fara dambe a tsakanin ɗaya daga cikin tsaffin masu yin sharar da wata sabuwar mai shara kan ta ga tana share titin da aka ware mata don ta rinƙa sharewa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Na buƙaci jin ba’asi, sai sabuwar shugabar mai kulawa da sabbin masu sharar ta ce min ai mu an dakatar da mu daga yin aiki, su ne yanzu aka ɗauka don su rinƙa yin aikin”.

“Bayan an kwana biyu, sai aka turo mana sakon karta kwana a wayoyinmu cewa wai an dakatar damu. A yanzu haka akasarinmu bashi ya yi mana katutu, wasun mu ma ba su da abincin da za su ciyar da iyalansu saboda ƙin biyanmu albashinmu.”

Ita ma wata mai aikin, Farida Nuhu ta ce, “A kullum da ƙarfe hudu na dare muke barin gidajenmu don zuwa yin aikin in ban da ranar Lahadi da hukumar ta ware a matsayin ranar hutunmu, kuma muna yin aikin ne a cikin hatsari, domin a yanzu haka akwai yaron da mota ta kaɗe shi yana kan aiki, dole muke fita da wuri kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna”.

Shi ma wani mai aikin, Idris Ashiru ya ce, ” Muna fitowa zuwa gun aikin da duku-duku ne, kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna, domin akwai wata mata mai aikin da mota ta kaɗe ta a babban titin Kawo har ta mutu, sannan akwai kuma wata a Kabala da mota ta taka ta, amma ba ta mutu ba, sai kuma wani mai aikin da mota ta kaɗe shi wanda a yanzu yana asibitin kwarraun na Shika an kwantar da shi. Komai ruwan sama ko sanyi, haka muke fitowa zuwa gun aikin, mu buƙatarmu ga gwamnatin shi ne, ta biya mu albashinmu kawai.”

Wakilinmu ya tuntubi shugaban masu kula da tsaftace muhalli da ke aiki a karkashin hukumar ta KCTA, Dakta Umar Lurwanu kan batun, inda ya ce, ba su da wata masaniya kan ɗaukar wasu sabbin masu aikin da kuma batun korar tsoffin masu yin aikin, amma maganar daga sama take, sannan suna yin dukkan mai yuwa don ganin an biya kowa hakkinsa.

Ya ce, “Ba mu san komai a kan yadda aka tsara ɗaukar sabbin ma’aikatan da kuma korar tsaffin ma’aikatan ba, mun gansu kawai son zo ƙofar hukumar suna zanga-zanga.

Kaduna
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.