ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Yi Zanga-Zanga A Kaduna -Masu Sharar Titi

by Abubakar Abba
2 years ago
Kaduna

Ɗaruruwan masu sharar manyan tititunan Jihar Kaduna, wanda akasarinsu mata ne da gwamnatin jihar ta ɗauka aiki sun gudanar da zanga-zangar lumana.

Sun yi zanga-zangar ce a kan gazawar gwamntin jihar na biyansu albashinsu na tsawon watanni biyar da kuma batun korar bazata da aka yi masu.

  • Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Fiye Da 200 A Kaduna – SEMA

Zanga-zangar ta gudana ne a ranar Litinin a wajen ƙofar hukumar raya birane mallakar gwamnatin Jihar Kaduna (KCTA), da ke a kan titin Ahmadu Bello.

ADVERTISEMENT

Sun yi zaman dirshan na wajen awa uku kan titin na Ahmadu Bello, inda hakan ya haifar da dakatar da zirga-zirgar ababen hawa wanda sai da Ƴansanda suka roƙe su, kafin suka bar kan titin.

Ɗaya daga cikin mai kulawa da masu yin sharar a titin Ali Akilu, Fatima Inusa ta shaida wa wakilinmu cewa, “Muna tsaka da aikin ba tare da umarni daga mahukuntan hukumar na cewa an dakatar da mu ba, sai muka ga an kawo wasu sabbin masu yin sharar, inda har aka fara dambe a tsakanin ɗaya daga cikin tsaffin masu yin sharar da wata sabuwar mai shara kan ta ga tana share titin da aka ware mata don ta rinƙa sharewa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Na buƙaci jin ba’asi, sai sabuwar shugabar mai kulawa da sabbin masu sharar ta ce min ai mu an dakatar da mu daga yin aiki, su ne yanzu aka ɗauka don su rinƙa yin aikin”.

“Bayan an kwana biyu, sai aka turo mana sakon karta kwana a wayoyinmu cewa wai an dakatar damu. A yanzu haka akasarinmu bashi ya yi mana katutu, wasun mu ma ba su da abincin da za su ciyar da iyalansu saboda ƙin biyanmu albashinmu.”

Ita ma wata mai aikin, Farida Nuhu ta ce, “A kullum da ƙarfe hudu na dare muke barin gidajenmu don zuwa yin aikin in ban da ranar Lahadi da hukumar ta ware a matsayin ranar hutunmu, kuma muna yin aikin ne a cikin hatsari, domin a yanzu haka akwai yaron da mota ta kaɗe shi yana kan aiki, dole muke fita da wuri kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna”.

Shi ma wani mai aikin, Idris Ashiru ya ce, ” Muna fitowa zuwa gun aikin da duku-duku ne, kafin motoci su fara zirga-zirga a kan tituna, domin akwai wata mata mai aikin da mota ta kaɗe ta a babban titin Kawo har ta mutu, sannan akwai kuma wata a Kabala da mota ta taka ta, amma ba ta mutu ba, sai kuma wani mai aikin da mota ta kaɗe shi wanda a yanzu yana asibitin kwarraun na Shika an kwantar da shi. Komai ruwan sama ko sanyi, haka muke fitowa zuwa gun aikin, mu buƙatarmu ga gwamnatin shi ne, ta biya mu albashinmu kawai.”

Wakilinmu ya tuntubi shugaban masu kula da tsaftace muhalli da ke aiki a karkashin hukumar ta KCTA, Dakta Umar Lurwanu kan batun, inda ya ce, ba su da wata masaniya kan ɗaukar wasu sabbin masu aikin da kuma batun korar tsoffin masu yin aikin, amma maganar daga sama take, sannan suna yin dukkan mai yuwa don ganin an biya kowa hakkinsa.

Ya ce, “Ba mu san komai a kan yadda aka tsara ɗaukar sabbin ma’aikatan da kuma korar tsaffin ma’aikatan ba, mun gansu kawai son zo ƙofar hukumar suna zanga-zanga.

Kaduna
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

Darasi Daga Suratul Fat’hi (3): Kowa Ya Yi Kokari Iya Karfinsa Wajen Girmama Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.