• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Nahuce

Abin al’ajabi a kan wata mata, a she a wannan zamani akwai mutane na gari masu imani da takawa sannan kuma ga tsoron Allah a wannan duniyar sannan kuma a wannan kasar ta mu Nijeriya.

Wata Hajiya da ke aikin hajjin bana a kasa mai tsarki wato kasar Saudiyya ta tsinci Dalar Amurka 80,000 wadda a kalla idan an canza ta a Naira a kudinmu na nan gida Nijeriya kudi ne masu tarin yawa, sannan kuma ta mika su ga hukuma domin a yi cigiyar mai su, kamar yadda cibiyar kula da Alhazai ta Jihar Sakkwato ta bayyana.

  • Tsohon Wakilin LEADERSHIP Ya Zama Shugaban Gidan Rediyon Kano
  • Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Matar mai suna Hajiya Aishatu ‘Yanguru Nahuce, asali daga Zamfara take, bayan ta tsinci wannan kudin ba ta bata lokaci ba ta mika su ga hukumar Alhazai ta jihar Zamfara domin a yi cikiyar mai kudin.

An yaba wa halayyar Hajiya Aishatu, kwararren dan jarida, Sakataran watsa labarai na shugaban jam’iyar PDP na kasa, Alhaji Yusuf Dingyadi ya ce, hakika wannan baiwar Allah ba karamin jihadi ta yi ba sannan kuma ba karamar karramawa da shaidar kwarai ta samu ba ga jama’a, musamman kasancewar ta mutunniyar kirki da ke tsoron Allah da kwadayin samun rahmar Allah. Allah ya saka mata da alheri.

Maruwaita rahotannin aikin hajji ne suka sanar da hakan cikin wani sako da suka wallafa a ranar Asabar a shafinsu na Facebook.

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Haka kuma, sun wallafa hoton Hajiyar wadda ta fito daga Karamar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara.

Muna rokon Allah ya ba ta ladan wannan gaskiya da amana da tsoran Allah da ta yi, sannan kuma Allah ya sa aikin hajjin da ta yi ya zama karbabbe Allah ya sa shi ne sanadin shigarta Aljannatul firdausi.

Tuni dai mabiya dandalin sada zumunta na Facebook suka rika bayyana ra’ayoyi mabambanta dangane da wannan baiwar Allah mai tausayi da tsoran Allah da ta yi abin a yaba mata.

A yayin da an samu masu yabawa ga wannan baiwar Allah da san kanta da ta yi daga tsoron azabar Allah ta mika wannan kudi ta san ba hakkin ta bane sannan kuma ta san idan ta ci su zai hana mata kwanciyar kabari da Hisabi shi ya sa ta mika su, a yayin da wasu kuma sun jefa ayar tambaya kan wai mai wani mahaluki zai yi da zunzurutun kudi har Dala 80,000?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
Ingantacciyar Hanyar Gyaran Gashi

Ingantacciyar Hanyar Gyaran Gashi

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.