• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Adon Gari
0
Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abin al’ajabi a kan wata mata, a she a wannan zamani akwai mutane na gari masu imani da takawa sannan kuma ga tsoron Allah a wannan duniyar sannan kuma a wannan kasar ta mu Nijeriya.

Wata Hajiya da ke aikin hajjin bana a kasa mai tsarki wato kasar Saudiyya ta tsinci Dalar Amurka 80,000 wadda a kalla idan an canza ta a Naira a kudinmu na nan gida Nijeriya kudi ne masu tarin yawa, sannan kuma ta mika su ga hukuma domin a yi cigiyar mai su, kamar yadda cibiyar kula da Alhazai ta Jihar Sakkwato ta bayyana.

  • Tsohon Wakilin LEADERSHIP Ya Zama Shugaban Gidan Rediyon Kano
  • Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Matar mai suna Hajiya Aishatu ‘Yanguru Nahuce, asali daga Zamfara take, bayan ta tsinci wannan kudin ba ta bata lokaci ba ta mika su ga hukumar Alhazai ta jihar Zamfara domin a yi cikiyar mai kudin.

An yaba wa halayyar Hajiya Aishatu, kwararren dan jarida, Sakataran watsa labarai na shugaban jam’iyar PDP na kasa, Alhaji Yusuf Dingyadi ya ce, hakika wannan baiwar Allah ba karamin jihadi ta yi ba sannan kuma ba karamar karramawa da shaidar kwarai ta samu ba ga jama’a, musamman kasancewar ta mutunniyar kirki da ke tsoron Allah da kwadayin samun rahmar Allah. Allah ya saka mata da alheri.

Maruwaita rahotannin aikin hajji ne suka sanar da hakan cikin wani sako da suka wallafa a ranar Asabar a shafinsu na Facebook.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Haka kuma, sun wallafa hoton Hajiyar wadda ta fito daga Karamar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara.

Muna rokon Allah ya ba ta ladan wannan gaskiya da amana da tsoran Allah da ta yi, sannan kuma Allah ya sa aikin hajjin da ta yi ya zama karbabbe Allah ya sa shi ne sanadin shigarta Aljannatul firdausi.

Tuni dai mabiya dandalin sada zumunta na Facebook suka rika bayyana ra’ayoyi mabambanta dangane da wannan baiwar Allah mai tausayi da tsoran Allah da ta yi abin a yaba mata.

A yayin da an samu masu yabawa ga wannan baiwar Allah da san kanta da ta yi daga tsoron azabar Allah ta mika wannan kudi ta san ba hakkin ta bane sannan kuma ta san idan ta ci su zai hana mata kwanciyar kabari da Hisabi shi ya sa ta mika su, a yayin da wasu kuma sun jefa ayar tambaya kan wai mai wani mahaluki zai yi da zunzurutun kudi har Dala 80,000?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajiya NahuceKudiSaudiyyaTsinta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun

Next Post

Ingantacciyar Hanyar Gyaran Gashi

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

1 month ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

7 months ago
Next Post
Ingantacciyar Hanyar Gyaran Gashi

Ingantacciyar Hanyar Gyaran Gashi

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.