ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
LEADERSHIP

Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron Kasa, Malam Nuhu Ribadu ya ba da tabbacin zai halarci babban taron Kamfanin LEADERSHIP na hadin gwiwa da NDLEA kan yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da sauran miyagun laifuka da rashin tsaro da kuma ci gaban kasa, a matsayin shugaban taron.

Taron mai taken, ‘Shan Miyagan Kwayoyi, Manyan Laifuka, Rashin Tsaro da Ci Gaban Kasa,’ wanda aka tsara gudanarwa a ranar 3 ga Agusta, 2023 a Babbar Cibiyar Taro ta Kasa da Kasa da ke Abuja, wani sabon yunkuri ne na shawo kan yawaitar bazuwar miyagun kwayoyin da ake fama da ita.

  • Yarjejeniyar Saukaka Zuba Jari Za Ta Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya Da Dala Triliyan 1
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Fitar Da Takin Zamani Da Hatsi Don Rage Radadin Cire Tallafin Fetur

Wata sanarwa da hukumar gudanarwar Rukunan Kamfanonin LEADERSHIP, mai dauke da sa hannun babban edita kuma babban mataimakin shugaban kamfanin, Mista Azu Ishiekwene, ta bayyana cewa kamfanin jaridun tare da hadin gwiwar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) sun dauki nauyin gudanar da taron ne, “domin samar da mafita kan matsalar a wannan zamani da ake kara bullo da sabbin fasahohi da hanyoyin safara da rarraba miyagun kwayoyin.”

ADVERTISEMENT

Ishiekwene ya kara da cewa taron na da nufin tattauna makomar yaki da miyagun kwayoyin ne bisa la’akari da yadda za a yi garambawul ga dokokin Nijeriya game da mallaka, amfani, hukunci, tarbiyyantarwa da kuma sake maido da wadanda kwaya ta tagayyara kan turba mai kyau.

“Kamar yadda binciken da Majalisar Dinkin Duniya ta yi kan amfani da kwayoyi a shekarar 2017, ya bayyana bisa kiyasi na adadin al’ummar Nijeriya miliyan 98, akwai miliyan 14.3 da ke amfani da miyagun kwayoyi.

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

“Wadannan alkaluma sun ninninka ba kawai bisa la’akari da karuwar jama’a da kuma yawan kalubalen zamantakewa da tattalin arziki ba, kai har ma da karuwar ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, da sauran munanan laifuka. Wannan abu ne mai ban tsoro kuma yana bukatar gudunmawa ta gaggawa daga dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren shugabannin Nijeriya da masu kishin kasa da kuma kamfanoni,” in ji sanarwar.

Ribadu, wanda ya kasance jagoran yaki da cin hanci da rashawa kuma shugaba na farko a hukumar yaki da masu zamba cikin aminci da karya tattalin arzikin kasa (EFCC), zai gabatar da jawabin bude taron a matsayinsa na shugaban taron.

Sanarwar ta kuma yi nuni da cewa, sabon mai ba wa shugaban kasar shawara a kan harkokin tsaron kasa (NSA) da ya zama na farko da aka nada a mukamin ba tare da ya taba yin aikin soja ba, tun bayan komawar mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999, zai kara tagomashi kan abubuwan da za a tattauna a taron sakamakon yadda a aikace ya fahimci dabarun tattara bayanan sirri da yaki da laifuffuka a lokacin da yake EFCC har ya yi suna a duniya ta wannan fuskar tare da samun lambobin yabo.

Ta kuma kara da cewa, a bisa la’akari da bukatar gaggauta kawar da barazanar shan muggan kwayoyi da ta’addanci, fashi da makami, da yadda abin ke illata ci gaban kasa, taron na hadin gwiwa tsakanin LEADERSHIP da NDLEA ya kudiri aniyar fayyace sabbin hanyoyin sarrafa kwayoyin, da fataucinsu da rarraba su, da kuma yin tambayoyi kan kokarin da hukumomin da ke sahun gaba a yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyin ke yi, tare da sake jaddada kiran shigar al’umma cikin lamarin.

Daga cikin manyan bakin da za su halarci taron akwai wadanda za su zo daga fadar shugaban kasa, majalisar dokoki ta kasa, sojoji, gwamnatocin jihohi, ma’aikatu da hukumomin gwamnati, sarakuna, jami’an diflomasiyya, hukumomin duniya, kamfanoni masu zaman kansu, malamai, kungiyoyi, Ofishin Majalisar Dinkin Duniya Mai Yaki da Miyagun Kwayoyi da Laifuffuka (UNODC), Sakatariyar Tarayyar Afirka da Ofishin Mai Ba Da Shawara Kan Tsaron Kasa (ONSA) da dai sauransu.

LEADERSHIP
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Next Post
Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

Musabbabin Haramta Sana'ar Gwangwan A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.