• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 5 Da Ke Sa Ido Fari Mai Ban Sha’awa

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
in Ado Da Kwalliya
0
Abubuwa 5 Da Ke Sa Ido Fari Mai Ban Sha’awa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu bibiyarmu a wannan shafi na Ado Da Kwalliya barkan mu da warhaka, barka da sake haduwa a wannan makon.

Duk lokacin da aka yi zancen farin ido ko mai hade da jajajaja galibin ‘yan’uwa mata sukan yi sha’awar a ce suna da shi saboda alama ce ta koshin lafiya da kuma abin da ake son gani a wurin ‘ya mace.

  • Zabtare Dala Miliyan 418 A Bashin Paris Club: Gwamnoni Sun Mayar Wa Malami Martani
  • Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

Yayin da ake kara girma, idanunmu kan sauya su ma, ba wai kawai wurin amfanin da suke mana ba har da yanayin kalarsu. Wasu za a ga idanunsu sun yi fatsi-fatsi, wasu rawaya-rawaya wasu kuma kan yi shudu-shudi.

Akan samu haka daga gado na iyaye da kakanni wasu kuma sanadin wani ciwo ne. A zahiri wasu ba su ba da kyawawan kulawa ga idanunsu, wasu kuma ba ma su yi kwata-kwata.

Idan idanu suna samun kyakkyawan kulawa, za a same su cikin koshin lafiya koyaushe. Abubuwa 5 da ke sa ido fari:

Labarai Masu Nasaba

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

  1. Kokwamba Wannan nau’in abinci an san shi da yawan ruwa a cikinsa, shi ya sa yake da karfi wajen taimaka wa gyara kalar ido ya zama fari. Har ila yau yana taimakawa wajen rage wani bakin kala da ake gani a ido musamman idan mutum ya gaji tibis. Idan kuna neman wani abu cikin sauki da ke sa ido fari, to ku rungumi amfani da kokwamba.
  2. Sanya wani abu mai sanyi a ido Amfani da wani abu mai sanyi a ido ba kawai yana taimakawa wajen kawar da kumburin ido ba ne, har ma yakan taimaka wajen mayar da ido ya zama fari. A rika tsoma tawul a ruwan sanyi ana matsawa a ido ko kuma a daura kankara a idon, za a sha mamaki. Idan aka rika matsa idon na tsawon minti 5 zuwa 10 na abin da aka sa mai sanyi na wasu lokuta a yini, ido zai yi fari abin sha’awa.
  3. Samun isasshen bacci na sa ido ya yi fari Samun isasshen bacci a kowane dare kamar na tsawon awa 7 zuwa 8 a kullum yana hutar da jijiyoyin idanu tare da dawo wa idon da kalar farin da yake da ita ta ainihi. Domin kara samun hutu yadda ya kamata da kuma mayar da farin ido, muna ba da shawara a rika wanka kafin a yi bacci.
  4. Amfani da ganyen shayi Ganyen shayi walau baki ko kore yana taka muhimmiyar rawa wajen sa hutu da kuma kara ingancin lafiyar ido. Idan ana amfani da ganyen shayi, idanu ba za su tsufa da wuri ba. Ganyen shayi na da matukar amfani wajen yaki da kwayoyin cututtuka da kuma abubuwan da ka iya sa idanu su yi ja.
  5. Yawaita shan kayan marmari da ganyayyaki Cin ganyayyaki na da matukar amfani wajen inganta lafiyar ido da kara masa fari. Haka nan shan kayan marmari.

Ko baya ga amfanin da kayan marmari da ganyayyaki ke yi ga ido, har ila yau sukan kuma taimaka wajen inganta lafiyar hanta da samun sinadarai masu amfani a jiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdoFariIdoKulawaKwalliyaKyauMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Siyasar Ubangida Da Zaben Shekarar 2023

Next Post

Tubabbun ‘Yan Ta’adda Sun Roki Yafiyar ‘Yan Nijeriya

Related

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata
Ado Da Kwalliya

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

1 week ago
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?
Ado Da Kwalliya

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

2 weeks ago
Ciwon Mara Lokacin Al’ada
Ado Da Kwalliya

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

2 weeks ago
Maganin Kurajen Fuska
Ado Da Kwalliya

Maganin Kurajen Fuska

4 weeks ago
Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?
Ado Da Kwalliya

Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?

1 month ago
Maganin Karin Kiba
Ado Da Kwalliya

Maganin Karin Kiba

1 month ago
Next Post
Tubabbun ‘Yan Ta’adda Sun Roki Yafiyar ‘Yan Nijeriya

Tubabbun 'Yan Ta'adda Sun Roki Yafiyar 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

May 31, 2025
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.