ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
9 months ago
Dabbobi

Gwanatin tarayya ta dauki matakin gaggawa na dakile yaduwar barkewar kwayoyin cutar kama kafafu da bakin dabbobi da ta bulla a wata gona da ake kiwon dabbobi a Birnin Kudu na Jihar Jigawa.

Ma’aikatar kula da bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya, ta bayyana haka ne a cikin sanawar da ta fitar.

  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sanarwar ta ce, ma’aiktar ta tura tawagar kwararrun likitoci takwas a karkashin jagorancin, Dakta Adeniyi Adedoyin, Darakta a sashen tsara ayyuka a ma’aikatar zuwa gonar ta kiwon dabbobin da ke Birnin Kudu, domin dakile yaduwar kwayoyin cutar.

ADVERTISEMENT

Daga cikin tawagar, akwai kuma wasu kwararru daga cibiyar gudanar da binciken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI) da wasu daga ma’aikatar ta kula da bunkasa kiwon dabbobi tare da taimakawar jami’an da ke kula da lafiya dabbobi ta Jigawa da kuma wasu shugabanni daga bangaren Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah.

Tawagar a gonar ta Mallam Alu Agro-Allied da annobar ta bulla, sun gano cewa; kimanin dabbobi 34 ne dauke da alamomin cutar, inda kuma tuni dabbobi shida da cutar ta harba, suka mutu.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Kazalika, tawagar ta kuma dauki alamomin kwayar cutar; domin yin gwajin tare kuma da kaddamar da yin Allurar rigafi ga dabbobin da ake kiwo da ke daura da gonar.

“Wannan matakin da aka dauka na gaggawa, ya nuna yadda ma’aikatar ta mayar da hankali, wajen tabbatar da kare lafiyar dabbobi, duba da cewa; fannin ne da ke kara taimakawa, wajen kara habaka tattalin arzikin kasar,” in ji Adedoyin.

“Ta hanyar aikin hadaka da muke ci gaba da gudanawa, muna kare hanyoyin sana’ar masu yin kiwon ne da kuma kara taimaka wa shirin shugaban kasa na sake farfado da fata, wato na ‘Renewed Hope Agenda’ tare kuma da shirin dabarun bunkasa kiwo na kasa (NLGAS),” a cewar Adedoyin.

Shi kuwa, Jami’i a Cibiyar Gudanar da Binciken Kula da Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) Hussain Ularamu, ya jaddada bukatar a rika kai rahoton bullar duk wata kwayar cuta ga hukumomin da suka kamata tare kuma da adana bayanan kwayoyin cutar, domin daukar matakan gaggawa.

Kazalika, a lokacin kai daukin, ma’aikatar ta wayar da kan Fulani Makiyaya da wasu masu kiwo, kan muhimmancin tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon dabbobinsu da kuma lokutan da ya kamata a rika yi wa dabbobin allurra rigakafi.

Su ma, a jawabansu daban-daban, Manajan Kula da Gonar Isa Mohammed Gadama da kuma Shugaban Kungiyar Miyetti Allah reshen jihar, Adamu Kankau, sun yaba wa gwamnatin tarayya kan daukin gaggawar da ta kawo a gonar, inda suka yi alkawarin ci gaba da bayar da hadin kai.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ma’aiktar Bunkasa Kiwon Dabbobi na Jihar Jigawa, Salem Abdurrahman, ya sanar da cewa; ma’aikatarsa, ta himmatu wajen gudanar da yi wa dabbobi allurar rigakafi a duk shekara tare kuma da ci gaba da sanya ido, kan bullar duk wata kwayar cuta da ke harbin dabbobi a jihar.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.