ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
7 months ago
Dabbobi

Gwanatin tarayya ta dauki matakin gaggawa na dakile yaduwar barkewar kwayoyin cutar kama kafafu da bakin dabbobi da ta bulla a wata gona da ake kiwon dabbobi a Birnin Kudu na Jihar Jigawa.

Ma’aikatar kula da bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya, ta bayyana haka ne a cikin sanawar da ta fitar.

  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sanarwar ta ce, ma’aiktar ta tura tawagar kwararrun likitoci takwas a karkashin jagorancin, Dakta Adeniyi Adedoyin, Darakta a sashen tsara ayyuka a ma’aikatar zuwa gonar ta kiwon dabbobin da ke Birnin Kudu, domin dakile yaduwar kwayoyin cutar.

ADVERTISEMENT

Daga cikin tawagar, akwai kuma wasu kwararru daga cibiyar gudanar da binciken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI) da wasu daga ma’aikatar ta kula da bunkasa kiwon dabbobi tare da taimakawar jami’an da ke kula da lafiya dabbobi ta Jigawa da kuma wasu shugabanni daga bangaren Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah.

Tawagar a gonar ta Mallam Alu Agro-Allied da annobar ta bulla, sun gano cewa; kimanin dabbobi 34 ne dauke da alamomin cutar, inda kuma tuni dabbobi shida da cutar ta harba, suka mutu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Kazalika, tawagar ta kuma dauki alamomin kwayar cutar; domin yin gwajin tare kuma da kaddamar da yin Allurar rigafi ga dabbobin da ake kiwo da ke daura da gonar.

“Wannan matakin da aka dauka na gaggawa, ya nuna yadda ma’aikatar ta mayar da hankali, wajen tabbatar da kare lafiyar dabbobi, duba da cewa; fannin ne da ke kara taimakawa, wajen kara habaka tattalin arzikin kasar,” in ji Adedoyin.

“Ta hanyar aikin hadaka da muke ci gaba da gudanawa, muna kare hanyoyin sana’ar masu yin kiwon ne da kuma kara taimaka wa shirin shugaban kasa na sake farfado da fata, wato na ‘Renewed Hope Agenda’ tare kuma da shirin dabarun bunkasa kiwo na kasa (NLGAS),” a cewar Adedoyin.

Shi kuwa, Jami’i a Cibiyar Gudanar da Binciken Kula da Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) Hussain Ularamu, ya jaddada bukatar a rika kai rahoton bullar duk wata kwayar cuta ga hukumomin da suka kamata tare kuma da adana bayanan kwayoyin cutar, domin daukar matakan gaggawa.

Kazalika, a lokacin kai daukin, ma’aikatar ta wayar da kan Fulani Makiyaya da wasu masu kiwo, kan muhimmancin tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon dabbobinsu da kuma lokutan da ya kamata a rika yi wa dabbobin allurra rigakafi.

Su ma, a jawabansu daban-daban, Manajan Kula da Gonar Isa Mohammed Gadama da kuma Shugaban Kungiyar Miyetti Allah reshen jihar, Adamu Kankau, sun yaba wa gwamnatin tarayya kan daukin gaggawar da ta kawo a gonar, inda suka yi alkawarin ci gaba da bayar da hadin kai.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ma’aiktar Bunkasa Kiwon Dabbobi na Jihar Jigawa, Salem Abdurrahman, ya sanar da cewa; ma’aikatarsa, ta himmatu wajen gudanar da yi wa dabbobi allurar rigakafi a duk shekara tare kuma da ci gaba da sanya ido, kan bullar duk wata kwayar cuta da ke harbin dabbobi a jihar.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.