ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
8 months ago
Dabbobi

Gwanatin tarayya ta dauki matakin gaggawa na dakile yaduwar barkewar kwayoyin cutar kama kafafu da bakin dabbobi da ta bulla a wata gona da ake kiwon dabbobi a Birnin Kudu na Jihar Jigawa.

Ma’aikatar kula da bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya, ta bayyana haka ne a cikin sanawar da ta fitar.

  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sanarwar ta ce, ma’aiktar ta tura tawagar kwararrun likitoci takwas a karkashin jagorancin, Dakta Adeniyi Adedoyin, Darakta a sashen tsara ayyuka a ma’aikatar zuwa gonar ta kiwon dabbobin da ke Birnin Kudu, domin dakile yaduwar kwayoyin cutar.

ADVERTISEMENT

Daga cikin tawagar, akwai kuma wasu kwararru daga cibiyar gudanar da binciken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI) da wasu daga ma’aikatar ta kula da bunkasa kiwon dabbobi tare da taimakawar jami’an da ke kula da lafiya dabbobi ta Jigawa da kuma wasu shugabanni daga bangaren Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah.

Tawagar a gonar ta Mallam Alu Agro-Allied da annobar ta bulla, sun gano cewa; kimanin dabbobi 34 ne dauke da alamomin cutar, inda kuma tuni dabbobi shida da cutar ta harba, suka mutu.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Kazalika, tawagar ta kuma dauki alamomin kwayar cutar; domin yin gwajin tare kuma da kaddamar da yin Allurar rigafi ga dabbobin da ake kiwo da ke daura da gonar.

“Wannan matakin da aka dauka na gaggawa, ya nuna yadda ma’aikatar ta mayar da hankali, wajen tabbatar da kare lafiyar dabbobi, duba da cewa; fannin ne da ke kara taimakawa, wajen kara habaka tattalin arzikin kasar,” in ji Adedoyin.

“Ta hanyar aikin hadaka da muke ci gaba da gudanawa, muna kare hanyoyin sana’ar masu yin kiwon ne da kuma kara taimaka wa shirin shugaban kasa na sake farfado da fata, wato na ‘Renewed Hope Agenda’ tare kuma da shirin dabarun bunkasa kiwo na kasa (NLGAS),” a cewar Adedoyin.

Shi kuwa, Jami’i a Cibiyar Gudanar da Binciken Kula da Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) Hussain Ularamu, ya jaddada bukatar a rika kai rahoton bullar duk wata kwayar cuta ga hukumomin da suka kamata tare kuma da adana bayanan kwayoyin cutar, domin daukar matakan gaggawa.

Kazalika, a lokacin kai daukin, ma’aikatar ta wayar da kan Fulani Makiyaya da wasu masu kiwo, kan muhimmancin tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon dabbobinsu da kuma lokutan da ya kamata a rika yi wa dabbobin allurra rigakafi.

Su ma, a jawabansu daban-daban, Manajan Kula da Gonar Isa Mohammed Gadama da kuma Shugaban Kungiyar Miyetti Allah reshen jihar, Adamu Kankau, sun yaba wa gwamnatin tarayya kan daukin gaggawar da ta kawo a gonar, inda suka yi alkawarin ci gaba da bayar da hadin kai.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ma’aiktar Bunkasa Kiwon Dabbobi na Jihar Jigawa, Salem Abdurrahman, ya sanar da cewa; ma’aikatarsa, ta himmatu wajen gudanar da yi wa dabbobi allurar rigakafi a duk shekara tare kuma da ci gaba da sanya ido, kan bullar duk wata kwayar cuta da ke harbin dabbobi a jihar.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.