• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana na ci gaba da fashin baki kan taron kolin da aka gudanar ka bunkasa tattalin arziki a tsakanin Afirka da Saudiyya da kuma Jamus.

A makon jiya ne aka gudanar da na Saudiyya, yayin da na Jamus kuma ya gudana a wannan makon.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

LEADERSHIP Hausa ta tattauna da Kwamared Sabo Muhammad, wani mai sharhin lamuran yau da kullum da ke jihar Bauchi kan alfanun wannan taron, inda ya yi bayani kan taron Saudiyya.

A cewarsa, “Shugaba Bola Ahmed Tinubu irin wannan damar yake bukata domin jawo kasashe masu arziki kamar Saudiyya su zo su sanya hannun jari a musamman bangaren man fetur da iskar gas da sauransu. Na biyu kuma taron zai kara inganta kasuwanci da Saudiyya da sauran kasashen Labarawa. Abu na uku kuma shi ne domin ya tabbatar wa Saudiyya da sauran kasashe da suke da zimmar zuba jari, cewa yanzu ‘Njeriya’ wata kasa ce sabuwa wadda kofarta take a bude da ake kira ‘Free Market economy’ cewa za ka zo ka yi kasuwancinka cikin sauki kuma idan ka sanya hannun jarinka za ka samu riba mai inganci sannan babu wasu tarnake-tarnake da ake da su a baya, misali na idan ka sanya kudi babu wata wahala za ka fitar da kudinka kasar waje kamar yadda muka gani a baya. Manya-manyan kamfanoni na jiragen sama sun daina hulda da Nijeriya kamar British Airways da kuma kamfanonin da suke Daular Larabawa da kasashe da dama saboda ba su iya samun kudadensu na  waje da ake biya ta dalar Amurka.

“A wannan ziyarar na shugaban kasa ya tattauna da Yarima mai jiran gado Bin Salman har ma Saudiyya ta ke da zimmar cewa nan ba da jimawa ba za ta sanya kusan dalar Amurka miliyan dari biyar shi ne kimanin riyal din Saudiyya miliyan dubu biyu a matatun man fetur na Nijeriya wanda gwamnati take da su guda hudu kuma za su sanya hannun a kan yarjejeniyar yadda za a karfafa alakar na sauran fannoni da suka shafi makamashi ta yadda za a karfafa wa kan yadda ake tafiyar da harkokin makamashi na zamani kuma shi ministan tattalin arziki na kasar Saudiyya ya ce nan da karshen wannan shekarar ko a zangon farko na shekarar da za mu shiga za a zo a yi jarjejeniya a sanya hannu.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

A cewar masanin, Bola Tinubu na kokari ne don tabbatar wa kasashen da yake ziyarta cewa, gwamnatin Nijeriya a karkashinsa tana bi dukkanin dokoki na kasuwanci na kasa da kasa kamar misalign shawarar da ya bi ta cire tallafin mai da kudin da ake narkawa wajen kare darajar Naira.

“Sannan na uku kuma, tunin a kan haraji an riga an yi kwamiti mai karfi wanda zai cire dukkanin wata sarkakiya na na haraji daban-daban da suke sanya wa kamfanoni masu hannun jarida. Da kuma bukatar da shi shugaban kasa ya ke da ita cewa su yi aiki da kasashen duniya musamman ita Saudiyya da sauran kasashen duniya musamman na Labarawa domin a samu a yaki matsalar tsaro ta yadda shi shugaba Tinubu ke son Nijeriya da Saudiyya su yi aiki tare domin yaki da akidun kungiyoyi irin su Boko Haram, ISWAP da sauransu da ke Nijeriya da yankin Chadi.”

“Abu na uku idan suka yi aiki tare a bangaren tsaro akwai akwai yiwuwar ita kasar Saudiyya za ta fi bai wa Nijeriya taimako na kayan aiki da kuma na kudade da canza bayanai na sirri tun da akwai ISIS a Nijeriya kuma ISIS suna da karfi a kasashen Labarawa ka ga Nijeriya za ta samu bayanan sirri daga wajen  Saudiyya domin dakile kungiyon ISIS-ISWAP da sauran kungiyoyin ta’addanci, shi ya sanya ma a ziyarar akwai mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribado da shugaban tattara bayanai na sirri Malam Abbakar, to dukka wadannan alkairi ne, amma gaskiya ba za a ga wadannan alkairan a yanzu-yanzu ba.” Ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Africa CDC Ya Yaba Da Hadin Gwiwar Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiyar Al’umma

Next Post

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

19 hours ago
Next Post
Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.