• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Ceto Daliban Kuriga

Tambayoyi Da Aka Gaza Amsawa Kan Sakin Daliban

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Ceto Daliban Kuriga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka sako daliban makarantar Kuriga 137 da ke Jihar Kaduna wanda suka yi garkuwa da su a makonni baya.

Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, ya bayyana cewa dalibai 137 ake yi garkuwa da su ba a ranar 7 ga Maris, 2024, a kauyen Kuriga da ke cikin karamar hukumar Chikun a jihar, ba dalibai 287 da ake ta yayatawa a kafafen yada labarai.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamnan ya bayyana adadin daliban ne a lokacin da yake zantawa da gidan talabijin Channels a shirin siyasa. Ya ce sojoji tare da hadin gwiwar jami’an tsaron sa-kai na Jihar Zamfara sun sami nasarar kubutar da dukkan daliban daga hannun ‘yan bindiga daga wuraren da suke rike da su.

Makonni hudu da suka wuce ne dai aka sace daliban daga makarantar firamare da sakandare ta Kuriga.

Shalkwatar tsaro ta bayyana cewa adadin dalibai guda 137 ne, ba kamar rahoton da ake bayyana na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai 287.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Sai dai kuma gwamnan ya yi takaicin mutuwar malamin makarantar a hannun masu garkuwan. Ya mika ta’aziyarsa ga iyalan da ‘yan’uwan malamin, sannan ya yi alkawarin mika daliban ga ‘ya’yansu.

Ya ce, “Mutum daya ne ya rasa ransa a hannun masu garkuwan shi ne malamin da suka tafi da shi, amma dukkan daliban guda 137 an samu nasarar ceto su cikin koshin lafiya. Muna takaicin abun da ya faru da malamin wanda jami’an tsaro su-ka bayyana mana cewa ba shi da lafiya, amma dukkan daliban an kubutar da su kuma suna hannunmu.”

Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa Sheikh Ahmad Gumi bai da hannu wajen ceto daliban, shehin malamin bai tattauna da ‘yan bindiga ba kafin sako daliban.

sai dai kuma masana na ganin cewa akwai tambayoyin da aka kasa amsawa wajen ceto daliban, kamar nawa aka biya ko kuma ba a bayar da kosisi ba? wani irin dubara aka bi wajen samun wannan nasara? Salun-alun ‘yan bindigan suka saki daliban ko sai da aka yi musayar wuta?

duk wadannan wasu tambayoyi ne wanda aka kasa amsawa game da ceto daliban Kuriga guda 137.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Next Post

Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

4 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

7 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

11 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

13 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

13 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

14 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.