• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Ceto Daliban Kuriga

Tambayoyi Da Aka Gaza Amsawa Kan Sakin Daliban

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kuriga

A makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka sako daliban makarantar Kuriga 137 da ke Jihar Kaduna wanda suka yi garkuwa da su a makonni baya.

Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, ya bayyana cewa dalibai 137 ake yi garkuwa da su ba a ranar 7 ga Maris, 2024, a kauyen Kuriga da ke cikin karamar hukumar Chikun a jihar, ba dalibai 287 da ake ta yayatawa a kafafen yada labarai.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamnan ya bayyana adadin daliban ne a lokacin da yake zantawa da gidan talabijin Channels a shirin siyasa. Ya ce sojoji tare da hadin gwiwar jami’an tsaron sa-kai na Jihar Zamfara sun sami nasarar kubutar da dukkan daliban daga hannun ‘yan bindiga daga wuraren da suke rike da su.

Makonni hudu da suka wuce ne dai aka sace daliban daga makarantar firamare da sakandare ta Kuriga.

Shalkwatar tsaro ta bayyana cewa adadin dalibai guda 137 ne, ba kamar rahoton da ake bayyana na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai 287.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Sai dai kuma gwamnan ya yi takaicin mutuwar malamin makarantar a hannun masu garkuwan. Ya mika ta’aziyarsa ga iyalan da ‘yan’uwan malamin, sannan ya yi alkawarin mika daliban ga ‘ya’yansu.

Ya ce, “Mutum daya ne ya rasa ransa a hannun masu garkuwan shi ne malamin da suka tafi da shi, amma dukkan daliban guda 137 an samu nasarar ceto su cikin koshin lafiya. Muna takaicin abun da ya faru da malamin wanda jami’an tsaro su-ka bayyana mana cewa ba shi da lafiya, amma dukkan daliban an kubutar da su kuma suna hannunmu.”

Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa Sheikh Ahmad Gumi bai da hannu wajen ceto daliban, shehin malamin bai tattauna da ‘yan bindiga ba kafin sako daliban.

sai dai kuma masana na ganin cewa akwai tambayoyin da aka kasa amsawa wajen ceto daliban, kamar nawa aka biya ko kuma ba a bayar da kosisi ba? wani irin dubara aka bi wajen samun wannan nasara? Salun-alun ‘yan bindigan suka saki daliban ko sai da aka yi musayar wuta?

duk wadannan wasu tambayoyi ne wanda aka kasa amsawa game da ceto daliban Kuriga guda 137.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.