ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Ceto Daliban Kuriga

Tambayoyi Da Aka Gaza Amsawa Kan Sakin Daliban

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kuriga

A makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka sako daliban makarantar Kuriga 137 da ke Jihar Kaduna wanda suka yi garkuwa da su a makonni baya.

Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, ya bayyana cewa dalibai 137 ake yi garkuwa da su ba a ranar 7 ga Maris, 2024, a kauyen Kuriga da ke cikin karamar hukumar Chikun a jihar, ba dalibai 287 da ake ta yayatawa a kafafen yada labarai.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamnan ya bayyana adadin daliban ne a lokacin da yake zantawa da gidan talabijin Channels a shirin siyasa. Ya ce sojoji tare da hadin gwiwar jami’an tsaron sa-kai na Jihar Zamfara sun sami nasarar kubutar da dukkan daliban daga hannun ‘yan bindiga daga wuraren da suke rike da su.

ADVERTISEMENT

Makonni hudu da suka wuce ne dai aka sace daliban daga makarantar firamare da sakandare ta Kuriga.

Shalkwatar tsaro ta bayyana cewa adadin dalibai guda 137 ne, ba kamar rahoton da ake bayyana na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai 287.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

Sai dai kuma gwamnan ya yi takaicin mutuwar malamin makarantar a hannun masu garkuwan. Ya mika ta’aziyarsa ga iyalan da ‘yan’uwan malamin, sannan ya yi alkawarin mika daliban ga ‘ya’yansu.

Ya ce, “Mutum daya ne ya rasa ransa a hannun masu garkuwan shi ne malamin da suka tafi da shi, amma dukkan daliban guda 137 an samu nasarar ceto su cikin koshin lafiya. Muna takaicin abun da ya faru da malamin wanda jami’an tsaro su-ka bayyana mana cewa ba shi da lafiya, amma dukkan daliban an kubutar da su kuma suna hannunmu.”

Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa Sheikh Ahmad Gumi bai da hannu wajen ceto daliban, shehin malamin bai tattauna da ‘yan bindiga ba kafin sako daliban.

sai dai kuma masana na ganin cewa akwai tambayoyin da aka kasa amsawa wajen ceto daliban, kamar nawa aka biya ko kuma ba a bayar da kosisi ba? wani irin dubara aka bi wajen samun wannan nasara? Salun-alun ‘yan bindigan suka saki daliban ko sai da aka yi musayar wuta?

duk wadannan wasu tambayoyi ne wanda aka kasa amsawa game da ceto daliban Kuriga guda 137.

Kuriga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Kuriga
Labarai

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Kuriga
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

LABARAI MASU NASABA

Kuriga

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Kuriga

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Kuriga

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Kuriga

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.