ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Ceto Daliban Kuriga

Tambayoyi Da Aka Gaza Amsawa Kan Sakin Daliban

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kuriga

A makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka sako daliban makarantar Kuriga 137 da ke Jihar Kaduna wanda suka yi garkuwa da su a makonni baya.

Gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, ya bayyana cewa dalibai 137 ake yi garkuwa da su ba a ranar 7 ga Maris, 2024, a kauyen Kuriga da ke cikin karamar hukumar Chikun a jihar, ba dalibai 287 da ake ta yayatawa a kafafen yada labarai.

  • Tsananin Zafin Rana Na Janyo Mana Cutar Daji – Shugaban Zabaya Na Kaduna
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

Gwamnan ya bayyana adadin daliban ne a lokacin da yake zantawa da gidan talabijin Channels a shirin siyasa. Ya ce sojoji tare da hadin gwiwar jami’an tsaron sa-kai na Jihar Zamfara sun sami nasarar kubutar da dukkan daliban daga hannun ‘yan bindiga daga wuraren da suke rike da su.

ADVERTISEMENT

Makonni hudu da suka wuce ne dai aka sace daliban daga makarantar firamare da sakandare ta Kuriga.

Shalkwatar tsaro ta bayyana cewa adadin dalibai guda 137 ne, ba kamar rahoton da ake bayyana na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai 287.

LABARAI MASU NASABA

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

Sai dai kuma gwamnan ya yi takaicin mutuwar malamin makarantar a hannun masu garkuwan. Ya mika ta’aziyarsa ga iyalan da ‘yan’uwan malamin, sannan ya yi alkawarin mika daliban ga ‘ya’yansu.

Ya ce, “Mutum daya ne ya rasa ransa a hannun masu garkuwan shi ne malamin da suka tafi da shi, amma dukkan daliban guda 137 an samu nasarar ceto su cikin koshin lafiya. Muna takaicin abun da ya faru da malamin wanda jami’an tsaro su-ka bayyana mana cewa ba shi da lafiya, amma dukkan daliban an kubutar da su kuma suna hannunmu.”

Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa Sheikh Ahmad Gumi bai da hannu wajen ceto daliban, shehin malamin bai tattauna da ‘yan bindiga ba kafin sako daliban.

sai dai kuma masana na ganin cewa akwai tambayoyin da aka kasa amsawa wajen ceto daliban, kamar nawa aka biya ko kuma ba a bayar da kosisi ba? wani irin dubara aka bi wajen samun wannan nasara? Salun-alun ‘yan bindigan suka saki daliban ko sai da aka yi musayar wuta?

duk wadannan wasu tambayoyi ne wanda aka kasa amsawa game da ceto daliban Kuriga guda 137.

Kuriga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

Xi Jinping Ya Taya Bassirou Diomaye Faye Murnar Zama Shugaban Senegal

LABARAI MASU NASABA

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.