ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

by Sadiq
2 years ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yi kira da aka yawan sojojin da aike jihar, domin magance ayyukan ‘yan bindiga.

Gwamnan ya ziyarci Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, a Hedikwatar tsaro da ke Abuja.

  • Mutane 11 Sun Rasu, 30 Sun Jikkata A Rikicin Kabilanci A Filato – Gwamnati
  • HOTUNA: Yadda Jami’an Tsaro Suka Lalata Haramtacciyar Matatar Danyen Mai A Ribas

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa Gwamnan ya gana da Babban Hafsan tsaron ne domin tattauna batun matsalar tsaro a Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

A yayin taron, Gwamna Lawal ya bayyana damuwarsa kan yadda ake ci gaba da kai hare-hare a wasu sassan Jihar Zamfara.

Ya kuma yi kira ga Babban Hafsan tsaron ƙasar da ya tura ƙarin sojoji da makaman da suka dace zuwa jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“A yau na zo nan ne domin tattaunawa kan matsalar rashin tsaro da ta addabi Jihar Zamfara. Na zo nan a ‘yan watannin da suka gabata saboda wannan batun.

“A ’yan kwanakin nan an sha fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga a wasu yankunan jihar.

“A cikin makon nan an kai wani hari a Ƙaramar Hukumar Tsafe, wanda ya yi sanadin asarar rayuka, ciki har da Jami’in Rundunar Kare Jama’a “Askarawan Zamfara” (CPG), sannan wasu ’yan bindiga sun ƙone motocin sojoji da suka haɗa da na jami’an CPG.

“Muna fama da ƙarancin sojoji a Zamfara saboda an sake tura wasu jami’an yankin Arewa maso Gabas.

“Manoma ba sa iya noma gonakinsu, kuma hare-haren da ake ci gaba da kaiwa ya janyo asarar rayuka da dama.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen kira gare ku da ku haɗa ƙarfi da ƙarfe domin tura ƙarin sojoji zuwa Zamfara, irin wannan mataki na da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da matsalar rashin tsaro da kuma dawo da zaman lafiya a jihar.

“Tsarin jami’an tsaro babu shakka zai kwantar wa jama’a hankali tare da karya gwiwar masu aikata laifuka daga aikata munanan ayyukansu.

Da yake mayar da martani, Babban Hafsan tsaron ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya yaba da ƙoƙarin Gwamna Lawal na yaƙi da ’yan bindiga a Zamfara.

Ya ce: “Ina godiya ga ƙoƙarin da ka ke yi na yaƙar rashin tsaro. Muna shirin daidaita al’amura a Zamfara kamar yadda muka yi a Maiduguri.

“Muna tattaunawa da dukkanin Kwamandoji da masu ruwa da tsaki don magance matsalar hare-haren, wanda ke matuƙar sanya ɓacin rai,” in ji Janar Musa.

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Muna Sane Nijeriya Ta Tsare Ɗan Kasarmu Ma’aikacin Binance – Amurka

Muna Sane Nijeriya Ta Tsare Ɗan Kasarmu Ma'aikacin Binance - Amurka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.