• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Za Ku Tsammaci Faruwarsu A 2024

by Azu Ishiekwene
2 years ago
in Bakon Marubuci
0
Abubuwan Da Za Ku Tsammaci Faruwarsu A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Za a cire tallafin man fetir, sannan akwai hasashen tashin gwauron zabo na farashin kaya tare da bukatar neman karin albashin ma’aikatan gwamnati daga shugabannin kungiyoyi wadanda sun san gaskiyar abin da ke faruwa, amma sai su yi kamar ba su sani ba. Har ila yau, wajen magance matsalar bambancin farashin Dala tsakanin na gwamnati da kuma kasuwar bayan fage, ana kyautata zaton wannan sabuwar gwamnati za ta sake yi wa farashin Dala kwaskwarima, inda farashin gwamnati zai kasance daga Naira 430-450 zuwa 550 a tashin farko”.

–Abin Da Kuka Yi Tsammani A 2023, Da ranar 29 Ga Disamba, 2022.

Wannan shi ne hasashena na hudu da na yi tun daga shekarar 2019. Baya ga wasu al’amura da suka faru, inda na tsinci kaina a wani yanayi maras dadi kamar lokacin annobar Korona da kuma abin mamakin da ya faru da Afirka a karshen wasan cin kwallon kafa ta duniya, maimakon Kasar Senegal ko Aljeriya sai ga Moroko a kan gaba, wannan ya sani sake kiyayewa yadda ya kamata.

A wannan shekara, zan fara ne da wasannin kwallon kafa. Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal a halin yanzu na cike da farin ciki tare da kwarin guiwa, amma me ya sa? Koda-yake dai wajibi ne su kara kaimi wajen yin kwazo, musamman ganin yadda suka kwashe shekaru ashiri ba tare da samun nasarar cin kofi ba.
Komai yana tafiya yadda ya kamata, domin kuwa kungiyar kwallon kafar na da kyakkyawan shiri tare da tsari, musamman idan aka yi la’akari da ‘yan wasansu masu kula da tsaron baya da kuma tsakiya dukkanninsu suna yin matukar kokari.

Har ila yau, labarin ba zai canza a wannan shekara ta 2024 ba. Ina fatan abin da ya faru da zukatan miliyoyin magoya baya shekaru ashirin da suka gabata, ba zai sake faruwa a nan gaba ba. Duk dai da cewa, yiwuwar kai bante ba a kan kungiyar kwallon kafar Arsenal din yake ba. Kungiyar na da matukar karfi, amma duk da haka tana samun rashin nasara a wasu lokutan.

Labarai Masu Nasaba

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Na fara da wasannin kwallon ne sakamakon ganin cewa, 2024 ba shekara ce ta hayaniyar siyasa a Nijeriya ba kamar yadda aka saba. A 2023, mun yi siyasar shekara hudu a cikin shekara guda. Baya ga wasu manyan Alkalai wadanda suke samun kudin shekara hudu a shekara guda kacal, inda wasu mashahuran ‘yan siyasar kuma ke karar da abin hannunsu tare da rabukewa guri guda. Saboda haka, ya zama wajibi a wannan shekara ta 2024 su fito ko ta halin kaka, domin ganin sun samu sun murmure don fita daga kangin da suke ciki, idan kuwa ba haka ko shakka babu za su yi asarar magoya bayansu baki-daya.

Kafin watan Yuli, wasu daga cikin manyan ‘yan siyasa wadanda suka iya riskar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu tare da neman alfarma a wurinsa, wadannan makomarsu na hannunsu; domin kuwa za su ci gaba da bayyana manufarsu da kuma rashin kunyarsu a fili. Kazalika zuwa karshen shekara kuma, alfarmar da shugaban kasar ke yi za ta tsaya cak, haka nan su ma ‘yan adawar sai kuma a shiga dimuwa.

Ko shakka babu Jihar Ido, Ondo da kuma Kano, Hukumar INEC ta kasa na shirye-shiryen sake wasu zabubbuka na ‘yan majalisar dattijai da na majalisar wakilai 11 da kuma majalisar jihohi 22. Fatan da nake yi ya kasance ba a samu abubuwan mamaki ba. Idan wani abu ya faru, ya kasance babbar jam’iyya mai mulki ta kasa (APC) ta karbe kujerun Sanatoci biyu ko uku, za ta kara samun karfi a majalisa, haka nan zai kasance a majalisar jihohi su ma.
A watan Satumba da Nuwamba, za a gudanar da zabubbuka a jihohi guda biyu, Jihar Edo da kuma Ondo.

Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki, wanda ya fara zangon mulkinsa a matsayin gwamnan APC, inda daga bisani ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP a zangonsa na biyu, yana yunkurin mika kujerar gwamnan ga wanda yake son ya gaje shi a jam’iyyar tasa ta PDP. Koda-yake dai, zabe ne kadai zai raba gaddama.

Har wa yau, a cikin jerin wadanda ke kan gaba wajen adawar siyasa a halin yanzu, Obaseki na kan gaba wajen fafatawa da tsohon mai gidansa Adams Oshiomhole, wanda a halin yanzu ke jam’iyyar APC a matsayin Sanata; sai kuma mai gidansa a halin yanzu, Nyesom Wike; guda daga cikin ministoci, wanda shi ba PDP ba, ba kuma dan jam’iyyar APC ba; da mataimakinsa Philip Shauib, wanda suka yi faman fafatawa tare da samun sabani har karshen zangon mulkin nasu.

Obaseki yana lissafa abubuwa da dama, daga cikinsu akwai batun son ya taimaka masa ya kai ga mika wa wanda yake so ya gaje shi a kujerarsa ta gwamna, tsohon Shugaban Bankin Sterlin, Asue Ighodalo.
Hasashena a nan, duk da kulle-kulle da tuggun irin na Obaseki, dan takararsa ba zai kai bantensa a zaben watan Satumba ba. abubuwan da ya shuka tsawon shekaru takwas, ko shakka babu su zai girba ko ya gani a kwaryar shansa a siyasance.

Babbar matsalar samun nasarar APC a wannan jiha, Adam Oshiomhole, sakamakon karkatar da dukkanin mukaman gwamnatin tarayya da aka yi zuwa Arewacin Jihar Edon, kawai don a bakanta wa wasu, bangaren kudanci kuma wadanda su ne matattarar zaben, akwai yiwuwar su fi karkata a kan jam’iyyar LP, wanda dan takarar ya fito daga yankinsu. Sai dai idan kuma dan takarar da APC ta tsayar ya zama mai matukar nagarta, hakan zai iya bayar da matukar mamaki.

A gefe guda kuma Jihar Ondo daban ce. Bayan tsawon watanni da aka shafe ana fafatawa da marigayi Gwamna Rotimi Akeredolu, inda a karshe Aiyedatiwa ya samu nasarar zama gwamnan rikon kwarya, yanzu kuma ya zama gwamna mai cikakken iko, yadda alamu suke nunawa zai iya faduwa zabe sakamakon kalubalen da ke waje da kuma ita kanta jam’iyyarsa.

Ya yi yakin neman zabensa da ya kamata ya yi nan gaba, amma yakin da ke tsakanin wannan lokaci zuwa watan Nuwamba, na tabbatar da cewa; ko shakka babu zai iya yin awon gaba da shi daga magoya bayan Akeredolu da kuma wasu daban, ciki har da Sanata Jimoh Ibrahim.

Abin da ya shafi Jihar Kano kuma, kotun koli ta bayyana daga nan har har zuwa 15 ga watan Janairu kafin ta kai ga yanke hukuncin. Har ila yau, tarihi ba zai taba manta wa da Gwamna Abba Kabir Yusuf ba, kamar yadda na fada a rubutun da na yi a baya, cikin shekara 20 da suka gabata; shari’u ‘yan kadan ne inda kotunan kasa suka yi hukunci iri guda kotun koli ta canza.

Shugaban Kasa Tinubu, ya yi matukar tayar da kura ta watanni bakwai da suka gabata, haka nan a wannan sabuwar shekara dole ya kara jajircewa tare da sanya idanu, musamman a kan abokanan aikinsa (ministoci), ta hanyar sauya wadanda bas u yi wani abin a zo a gani ba, yayin da yake cika shekara daya a kan karagar mulki.
Sannan, babban kalubalen da zai ci gaba da fuskanta shi ne batun tattalin arziki, musamman ganin yadda hauhawar farashi ya karu da kashi 27.3, darajar naira ta fadi da kashi 50 cikin 100 cikin wata shida, rashin aikin yi ke ci gaba da ta’azzara, don haka duk abin da aka samu a 2024 ba zai isa ba, sai an samu gibi.

Yanzu haka, naira ta kasa tsayuwa da kafafunta, tana daf da kullewa a kan 1500 kowace dala a kasuwar bayan fage, don haka sai dai idan an yi matukar sa’a man fetir da gas sun matukar tashi, sannan za a samu saukin al’amuran.

Abu na biyu kuma shi ne batun noma ta yadda za a samu farashin kayan abinci ya sauko daga kashi 32 da yake a halin yanzu, ta hanyar samun damuna mai albarka tare kuma da samun wadataccen tsaro a fadin kasa baki-daya, su ne za su taimaka wajen bunkasar samun abinci.

Bugu da kari, babbar matsalar da Babban Bankin Nijeriya ya ke da shi, idan aka ajiye batun alkawarin da ya yi na kokarin daidaita farashi a 2024, rahoton da mai gudanar da bincike ya gabatar ya shafe komai da komai.
Haka zalika, ka da a yi tsammanin samun wadatacciyar wutar lantarki saboda dalili guda: ko da gurare hudu da ke samar wa da Nijeriya wutar lantarki za su iya sama mata sama da mega wat dubu 2 kowannensu, wanda hakan ma ba zai taba yiwuwa ba, ba a taba samun wadatacciyar wuta ba.

Haka nan, batun samar da gas, batu na gaskiya shi ne babu gas din. Sannan, kamfanin gas din na Nijeriya bashi ya yi masa katutu, har ila yau, yanayin kasuwa kuma ya dakile ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

Haka nan, duk wanda ke tsamnin za a samu sauki a harkar shigo da man fetir ko samun saukin farashi, wani abu ne wanda za a jima ana jira. Sannan, batun gyara matatun man fetir, shi ma abu ne da sai ya dauki lokaci, matatar mai ta Dangote kuma ba ta iya bayar da wadataccen man da ke bukata ba, sai bayan wani lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2024DuniyaNigeriaShugaba Tinubusiyasar Nijeriyazabubbukan 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyfatin Na Ƙasar Ghana ANDRE AYEW Na Fatan Kafa Tarihi A Gasar AFCON Ta Bana

Next Post

EFCC Ba Samame Ta Kai Mana Ba – Dangote

Related

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

3 weeks ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

4 weeks ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

2 months ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

2 months ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 months ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

3 months ago
Next Post
Efcc

EFCC Ba Samame Ta Kai Mana Ba - Dangote

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.