• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

by Sani Anwar
1 year ago
in Kiwon Lafiya
0
Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

Muslim devotees pray before breaking their fast along a street during the holy month of Ramadan in Peshawar on March 27, 2023. (Photo by Abdul MAJEED / AFP) (Photo by ABDUL MAJEED/AFP via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yake kusan al’ummar musulmi a duk duniya sun fara Azumin Ramadan na bana, yana da kyau a rika lura da kiwon lafiya musamman da a wannan shekarar ake gudanar da azumin da bazara, lokacin tsananin zafi.

-Ka da mai Azumi ya yi wasa da shan ruwa lokacin bude-baki. Da zarar lokacin bude-baki ya yi, ya gaggauta shan ruwa kafin ya kai ga cin abinci, sannan ya kamata ya kula; ka da ya take cikinsa da ruwa ta yadda cikin nasa zai kulle; har ta kai shi ga yin amai.

  • Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya
  • Ana Amfani Da Na’urar Hakar Mai Ta Zamani Da Kamfanin Sin Ya Kera A Uganda

-Ana bukatar mai Azumi ya ci nau’ikan abinci iri daban-daban bayan shan ruwa, dalili kuwa; jikinsa na bukatar abinci mai kyau, wanda zai maye gurbin abin da ya rasa sakamakon wannan Azumi da ya yi. Don haka, akwai bukatar cin abinci mai kyau da kayan marmari da sauran abin da ya shafi dangin ganyayyaki, wadanda za su kara masa lafiyar jiki.

-Haka nan, ka da mai Azumi ya rika cin abinci ya na take cikinsa a lokacin shan ruwa. A tsaya a ci abinci a tsanake, ta yadda za a kawar da yunwa ba tare da an yi cin da zai iya cutarwa ba.

-Sannan, a rika dan motsa jiki bayan shan ruwa, duk dai da cewa, ba za a ba da shawarar a rika motsa jiki da safe ko rana ko kuma yamma ba, saboda yanayin kishirwa da ake fama da ita, amma duk da haka; bayan shan ruwa ka da a lafke, a dan yi kokari a rika dan kai-komo.

Labarai Masu Nasaba

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

-A rika kwantawa ana samun isasshen barci, domin samun kuzari da kuma lafiyar jiki baki-daya.

-Har ila yau, da yake jiki iri daban-daban ne, idan ka jarraba wadannan shawarwari da muka bayar ka ji jikinka bai yi maka yadda kake so ba, tun wuri ka dakata kar ka ci gaba, kana iya samun likitanka; ya ba ka shawara a kan abin da ya fi dacewa da kai.

Haka zalika, ka da a manta cewa; wannan wata shi ne wanda musulmi suka fi so a rayuwarsu baki-daya; inda suke haduwa da mutane daban-daban su ci abinci tare, masu shi su taimaka wa marasa shi tare da kyautata ibada da kuma kara tsoron Allah a lokaci guda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarabar Girke-girken Azumi

Next Post

Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

Related

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

3 hours ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

14 hours ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

3 weeks ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

4 weeks ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

2 months ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Next Post
Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

LABARAI MASU NASABA

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.