ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Zogale Ga Lafiyar Jikin Ɗan’adam

by Sani Anwar
6 months ago
Zogale

Masana harkokin lafiyar abinci, sun bayyana amfanin da ganyen zogale ke da shi a jikin Ɗan’adam, sakamakon sinadarin da yake ƙunshe da su.

Har ila yau, bincike ya tabbatar da cewa; zogale yana da matuƙar albarka, domin kuwa ya kan fito har a wurin da babu ruwa.

  • Kasar Sin Ta Zama Babbar Kasuwar Da Fim Din “Zootopia 2” Ya Samu Kudi
  • Farfesa Gwarzo Ya Gwangwaje Cibiyar Ilimi ‘Alliance Française Kano’ Da Gini Mai Hawa Biyu Na Zamani

Don haka, ganyensa da sassaƙensa; na da matuƙar amfani a jikin mutum. Sannan kuma, yana ɗauke da sinadarin A.B.C.D har ma da E, kana kuma yana ɗauke da sinadarin calcium da potassium, kazalika kuma; mansa yana cikin mayukan da suka fi tsada a duniya.

ADVERTISEMENT

Kazalika, akwai magunguna 18 da zogale ke yi ga lafiyar Ɗan’adam kamar haka:

-Ana dafa ganyen zogale da zuma a sha kamar shayi, domin maganin Olsa (Ulcer).

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

-Ana kuma shafa ɗanyen ganyen zogale a kan goshi, don maganin ciwon kai.

-Haka nan, ga wanda ya ji wani rauni ko sara; idan ya shafa ɗanyen ganyen zogale, jinin zai tsaya nan take da izinin Allah.

-Ga mai fama da ƙurajen jiki, sai ya haɗa garin zogale da man zaitun; ya riƙa shawa.

-Ana kuma zuba garin zogale a kan gyambo ko wani rauni, domin ya yi saurin warkewa.

-Sanya garin zogale a cikin abinci, na maganin hawan jini da kuma ƙara wa mutum kuzari,

-Ana dafa ganyen zogale, a saka kanwa ‘yar kaɗan; don maganin shawara.

-Ga mai fama da ciwon ido, zai riƙa ɗiga ruwan ɗanyen zogale; haka nan, shi ma mai fama da ciwon kunne.

-Macen da ke shayarwa kuma, sai ta dafa furen zogale da zuma; domin samun ƙarin yawan ruwan nono.

-Wanda ke fama da yawan fitsari ko ciwon Siga, sai ya riƙa shan furen zogale da citta kamar shayi.

-Kazalika, cin zogalen ma a haka; na maganin tsutsar ciki, musamman ga yara ƙanana.

-Ana daka ganyen  zogale da ‘ya’yan ɓaure a sha da nono ko kunu, domin kuwa yana maganin ciwon hanta.

-Ga mai fama da sanyin ƙashi ko wani kumburi, sai ya soya ‘ya’yan zogale ya daka su; ya kuma haɗa da man kwakwa (man- ja) sai ya riƙa shafawa.

-A daka zangarniyar zogale da ‘ya’yan da ke ciki da kaninfari, citta, masoro da kuma kimba, domin ƙarin ƙarfin namiji, sannan yana ƙara wa mata nishaɗi.

-A daka saiwar zogale da ‘ya’yan kankana a sha a nono, yana maganin tsakuwar ciki (Apendis).

-Haka nan, yana maganin typhoid, maleriya, basir da shawara; ta hanyar yawan shan ruwan dafaffen zogale.

-Kazalika, zogale na rage raɗaɗin ciwon HIV ta hanyar shan dafaffen ruwan zogalen.

Zogale
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Harin Ƴan Bindiga Ya Halaka Mutum 11 A Pretoria

Harin Ƴan Bindiga Ya Halaka Mutum 11 A Pretoria

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.