• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Abun Da Aka Shuka Shi Za A Girba!
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani sakamakon bincike na jin raayin alumma, da jaridar The Guardian ta Amurka ta wallafa a baya bayan nan, ya nuna yadda duk cikin Amurkawa biyar, daya daga cikinsu ke ganin abu ne mai kyau, a cimma burin siyasa ta hanyar tarzoma.

Ko shakka babu hakan abun tsoro ne, da tayar da hankali, ganin cewa wannan tunani ya yi hannun riga da ainihin tushen dimokaradiyya, wanda ya tanadi cimma duk wani buri ta maslaha da kwanciyar hankali.

  • Sin Ta Mayar Da Martani Ga Rahoton Shekara-shekara Na Fataucin Bil Adama Na Amurka

Wani abun lura game da wannan bincike, shi ne yadda Amurkawa ke saurin yarda da farfagandar ’yan siyasa, wadda ke haifar da rashin yarda, da nuna kyama, da amincewa daukar matakan tada zaune tsaye, yayin da suke son cimma wani buri na siyasa ko zamantakewa.

Ko da yake dai Bahaushe kan ce Barewa ba za ta yi gudu dan ta ya yi rarrafe ba. Duniya ta ga misalin irin wannan tunani tun daga kan jagororin Amurka, inda alal misali, a ranar 6 ga watan Janairun shekarar bara, daruruwan magoya bayan tsohon shugaban kasar Donald Trump, suka yi kutse cikin ginin majalissar dokokin kasar na Capitol, da nufin hana bayyana tsohon shugaban kasar a matsayin wanda ya sha kaye a babban zaben da ya gabata.

Wanda hakan ya sabbaba rasuwar mutane 7 da jikkatar gwamman mutane. Masu bibiyar lamarin sun tabbatar da cewa shi kansa tsohon shugaba Trump, ya nuna wasu alamu na goyon bayan wancan kutse.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Masharhanta dai na ganin idan har wannan yanayi na yin watsi da tushen dimokaradiyya ya ci gaba da kamari a Amurka, mai yiwuwa kasar ta fuskanci manyan bore masu nasaba da siyasa a nan da ’yan shekaru masu zuwa.

Domin kaucewa hakan, wajibi ne jagororin kasar su yi karatun ta-nutsu, su yi hangen nesa wajen wayar da kan Amurkawa, game da illar dake tattare da daukar doka a hannu, da kin amincewa da mabanbantan raayoyi, da nuna isa, wadanda dukkaninsu munanan dabiu ne da ka iya haifarwa kasar da maras ido.

Uwa uba kuma, ya zama wajibi gwamnatin Amurka ta dawo daga rakiyar manufarta ta shiga sharo ba shanu, da nuna karfin tuwo ga sauran kasashe, ko nuna kyama ga hanyoyin ci gaba da sauran kasashe suka zabawa kan su, domin kuwa irin wannan tunani ne ke haifarwa ’yan kasar ta yanayi na kangarewa, da kin karbar gaskiya!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ba Za Ta Iya Bata Sunan Xinjiang Ba

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Related

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

19 hours ago
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

20 hours ago
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

22 hours ago
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

22 hours ago
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

1 day ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Zartar Da Dokar Hana Acaba

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar KarÉ“ar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar KarÉ“ar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar ÆŠalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar ÆŠalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce KaÉ—ai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce KaÉ—ai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.