• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa

bySadiq
2 years ago
ACG

Kungiyar hadin kan kasashen Larabawa (ACG) ta sanar da cewa za ta ware kudi har dala biliyan 50, don taimakawa wajen samar da ababen more rayuwa a nahiyar Afirka.

Shugaban bankin ci gaban Musulunci, Dokta Muhammad Al Jasser ne ya sanar da hakan a taron tattalin arzikin kasashen Larabawa da Afirka da aka gudanar a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

  • Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya
  • Xi Ya Amsa Wasikar Da Matias TarnopolskyTarnopolsky Ya Rubuta Masa

Kasashe da yawa a Afirka na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

A cikin sanarwar hadin gwiwa, kungiyar ta ce: “Duba da alakar da ke tsakaninmu za mu samar da abubuwan ci gaba masu dorewa da kuma samar da kudade don inganta sauyin yanayi.

“Yarjejeniyar da kuma taimakawa wajen cike gibin zuba jari a fannin samar da makamashi, da suka hada da karancin makamashin ‘carbon’, daidaita sauyin yanayi da kuma samar da abinci.”

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Bayar da tallafin ACG zai tallafa wa shirye-shirye a fannoni kamar tsaro na makamashi da canjin makamashi, hadin kai a nahiyar, harkokin kasuwanci, shirye-shiryen jinsi da matasa, samar da kudade da sauran ababen more rayuwa.

A cikin sanarwar ta ACG ta ce “Mun amince da bukatar magance wadannan kalubale ta hanyar daukar matakan da suka dace a kan lokaci.”

A madadin kungiyar ta ACG, Al Jasser ya ce: “Tabbas a shirya muke mu cika alkawarin da muka daukar wa Afirka.”

“Duk da haka, muna sane da kalubalen ci gaban da nahiyar ke fuskanta – illar da cutar COVID-19 ta haifar a duniya a baya-bayan nan, da kalubalen samar da abinci, da kuma kara tabarbarewar tattalin arziki.

“Mun himmatu wajen yin aiki kafada da kafada da kasashen Afirka da kungiyoyin jama’a, da kamfanoni masu zaman kansu, da sauran cibiyoyin raya kasa.”

Kungiyar ta kasance mai goyon bayan kasashen Afirka da dama kuma ta zuba jarin sama da dalar Amurka biliyan 220 a yankin zuwa yanzu.

Sanarwar ta kara da cewa, “Mun sake jaddada aniyarmu na tallafa wa ci gaban kasashen Afirka.”

Mambobin kungiyar sun hada da Asusun Raya Abu Dhabi, Bankin Larabawa don Ci gaban Tattalin Arziki a Afirka, Asusun Larabawa don Ci Gaban Tattalin Arziki da Ci Gaban Al’umma, Shirin Raya Gabas na Larabawa, Asusun Lamuni na Larabawa, Bankin Raya Islama, Asusun Kuwait. Bunkasa Tattalin Arziki, Asusun OPEC na Ci Gaban Ƙasashen Duniya, Asusun Raya Kasar Qatar da Asusun Raya Kasar Saudiyya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Kwastam

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version