• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar hadin kan kasashen Larabawa (ACG) ta sanar da cewa za ta ware kudi har dala biliyan 50, don taimakawa wajen samar da ababen more rayuwa a nahiyar Afirka.

Shugaban bankin ci gaban Musulunci, Dokta Muhammad Al Jasser ne ya sanar da hakan a taron tattalin arzikin kasashen Larabawa da Afirka da aka gudanar a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

  • Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya
  • Xi Ya Amsa Wasikar Da Matias TarnopolskyTarnopolsky Ya Rubuta Masa

Kasashe da yawa a Afirka na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

A cikin sanarwar hadin gwiwa, kungiyar ta ce: “Duba da alakar da ke tsakaninmu za mu samar da abubuwan ci gaba masu dorewa da kuma samar da kudade don inganta sauyin yanayi.

“Yarjejeniyar da kuma taimakawa wajen cike gibin zuba jari a fannin samar da makamashi, da suka hada da karancin makamashin ‘carbon’, daidaita sauyin yanayi da kuma samar da abinci.”

Labarai Masu Nasaba

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Bayar da tallafin ACG zai tallafa wa shirye-shirye a fannoni kamar tsaro na makamashi da canjin makamashi, hadin kai a nahiyar, harkokin kasuwanci, shirye-shiryen jinsi da matasa, samar da kudade da sauran ababen more rayuwa.

A cikin sanarwar ta ACG ta ce “Mun amince da bukatar magance wadannan kalubale ta hanyar daukar matakan da suka dace a kan lokaci.”

A madadin kungiyar ta ACG, Al Jasser ya ce: “Tabbas a shirya muke mu cika alkawarin da muka daukar wa Afirka.”

“Duk da haka, muna sane da kalubalen ci gaban da nahiyar ke fuskanta – illar da cutar COVID-19 ta haifar a duniya a baya-bayan nan, da kalubalen samar da abinci, da kuma kara tabarbarewar tattalin arziki.

“Mun himmatu wajen yin aiki kafada da kafada da kasashen Afirka da kungiyoyin jama’a, da kamfanoni masu zaman kansu, da sauran cibiyoyin raya kasa.”

Kungiyar ta kasance mai goyon bayan kasashen Afirka da dama kuma ta zuba jarin sama da dalar Amurka biliyan 220 a yankin zuwa yanzu.

Sanarwar ta kara da cewa, “Mun sake jaddada aniyarmu na tallafa wa ci gaban kasashen Afirka.”

Mambobin kungiyar sun hada da Asusun Raya Abu Dhabi, Bankin Larabawa don Ci gaban Tattalin Arziki a Afirka, Asusun Larabawa don Ci Gaban Tattalin Arziki da Ci Gaban Al’umma, Shirin Raya Gabas na Larabawa, Asusun Lamuni na Larabawa, Bankin Raya Islama, Asusun Kuwait. Bunkasa Tattalin Arziki, Asusun OPEC na Ci Gaban Ƙasashen Duniya, Asusun Raya Kasar Qatar da Asusun Raya Kasar Saudiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ACGAfrikaLabarawaSaudiyyaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

Related

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

3 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

5 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

5 hours ago
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

6 hours ago
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
Labarai

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

8 hours ago
Next Post
Kwastam

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

LABARAI MASU NASABA

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.