• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar hadin kan kasashen Larabawa (ACG) ta sanar da cewa za ta ware kudi har dala biliyan 50, don taimakawa wajen samar da ababen more rayuwa a nahiyar Afirka.

Shugaban bankin ci gaban Musulunci, Dokta Muhammad Al Jasser ne ya sanar da hakan a taron tattalin arzikin kasashen Larabawa da Afirka da aka gudanar a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

  • Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya
  • Xi Ya Amsa Wasikar Da Matias TarnopolskyTarnopolsky Ya Rubuta Masa

Kasashe da yawa a Afirka na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

A cikin sanarwar hadin gwiwa, kungiyar ta ce: “Duba da alakar da ke tsakaninmu za mu samar da abubuwan ci gaba masu dorewa da kuma samar da kudade don inganta sauyin yanayi.

“Yarjejeniyar da kuma taimakawa wajen cike gibin zuba jari a fannin samar da makamashi, da suka hada da karancin makamashin ‘carbon’, daidaita sauyin yanayi da kuma samar da abinci.”

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Bayar da tallafin ACG zai tallafa wa shirye-shirye a fannoni kamar tsaro na makamashi da canjin makamashi, hadin kai a nahiyar, harkokin kasuwanci, shirye-shiryen jinsi da matasa, samar da kudade da sauran ababen more rayuwa.

A cikin sanarwar ta ACG ta ce “Mun amince da bukatar magance wadannan kalubale ta hanyar daukar matakan da suka dace a kan lokaci.”

A madadin kungiyar ta ACG, Al Jasser ya ce: “Tabbas a shirya muke mu cika alkawarin da muka daukar wa Afirka.”

“Duk da haka, muna sane da kalubalen ci gaban da nahiyar ke fuskanta – illar da cutar COVID-19 ta haifar a duniya a baya-bayan nan, da kalubalen samar da abinci, da kuma kara tabarbarewar tattalin arziki.

“Mun himmatu wajen yin aiki kafada da kafada da kasashen Afirka da kungiyoyin jama’a, da kamfanoni masu zaman kansu, da sauran cibiyoyin raya kasa.”

Kungiyar ta kasance mai goyon bayan kasashen Afirka da dama kuma ta zuba jarin sama da dalar Amurka biliyan 220 a yankin zuwa yanzu.

Sanarwar ta kara da cewa, “Mun sake jaddada aniyarmu na tallafa wa ci gaban kasashen Afirka.”

Mambobin kungiyar sun hada da Asusun Raya Abu Dhabi, Bankin Larabawa don Ci gaban Tattalin Arziki a Afirka, Asusun Larabawa don Ci Gaban Tattalin Arziki da Ci Gaban Al’umma, Shirin Raya Gabas na Larabawa, Asusun Lamuni na Larabawa, Bankin Raya Islama, Asusun Kuwait. Bunkasa Tattalin Arziki, Asusun OPEC na Ci Gaban Ƙasashen Duniya, Asusun Raya Kasar Qatar da Asusun Raya Kasar Saudiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ACGAfrikaLabarawaSaudiyyaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

2 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

4 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

4 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

9 hours ago
Next Post
Kwastam

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.