ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACG Za Ta Tallafa Wa Afrika Da Dala Biliyan 50 Don Samar Da Ababen More Rayuwa

by Sadiq
3 years ago
ACG

Kungiyar hadin kan kasashen Larabawa (ACG) ta sanar da cewa za ta ware kudi har dala biliyan 50, don taimakawa wajen samar da ababen more rayuwa a nahiyar Afirka.

Shugaban bankin ci gaban Musulunci, Dokta Muhammad Al Jasser ne ya sanar da hakan a taron tattalin arzikin kasashen Larabawa da Afirka da aka gudanar a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

  • Dokar Fallasa Barayin Gwamnati Na Nan Daram – Gwamnatin Tarayya
  • Xi Ya Amsa Wasikar Da Matias TarnopolskyTarnopolsky Ya Rubuta Masa

Kasashe da yawa a Afirka na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar hadin gwiwa, kungiyar ta ce: “Duba da alakar da ke tsakaninmu za mu samar da abubuwan ci gaba masu dorewa da kuma samar da kudade don inganta sauyin yanayi.

“Yarjejeniyar da kuma taimakawa wajen cike gibin zuba jari a fannin samar da makamashi, da suka hada da karancin makamashin ‘carbon’, daidaita sauyin yanayi da kuma samar da abinci.”

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Bayar da tallafin ACG zai tallafa wa shirye-shirye a fannoni kamar tsaro na makamashi da canjin makamashi, hadin kai a nahiyar, harkokin kasuwanci, shirye-shiryen jinsi da matasa, samar da kudade da sauran ababen more rayuwa.

A cikin sanarwar ta ACG ta ce “Mun amince da bukatar magance wadannan kalubale ta hanyar daukar matakan da suka dace a kan lokaci.”

A madadin kungiyar ta ACG, Al Jasser ya ce: “Tabbas a shirya muke mu cika alkawarin da muka daukar wa Afirka.”

“Duk da haka, muna sane da kalubalen ci gaban da nahiyar ke fuskanta – illar da cutar COVID-19 ta haifar a duniya a baya-bayan nan, da kalubalen samar da abinci, da kuma kara tabarbarewar tattalin arziki.

“Mun himmatu wajen yin aiki kafada da kafada da kasashen Afirka da kungiyoyin jama’a, da kamfanoni masu zaman kansu, da sauran cibiyoyin raya kasa.”

Kungiyar ta kasance mai goyon bayan kasashen Afirka da dama kuma ta zuba jarin sama da dalar Amurka biliyan 220 a yankin zuwa yanzu.

Sanarwar ta kara da cewa, “Mun sake jaddada aniyarmu na tallafa wa ci gaban kasashen Afirka.”

Mambobin kungiyar sun hada da Asusun Raya Abu Dhabi, Bankin Larabawa don Ci gaban Tattalin Arziki a Afirka, Asusun Larabawa don Ci Gaban Tattalin Arziki da Ci Gaban Al’umma, Shirin Raya Gabas na Larabawa, Asusun Lamuni na Larabawa, Bankin Raya Islama, Asusun Kuwait. Bunkasa Tattalin Arziki, Asusun OPEC na Ci Gaban Ƙasashen Duniya, Asusun Raya Kasar Qatar da Asusun Raya Kasar Saudiyya.

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Next Post
Kwastam

Kwastam Ta Kwace Tirelar Shinkafa 13 Da Kayan Naira Bilyan 1.2

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.