• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adawar Siyasa: ‘Yan Siyasa Sun Fara Kewaya Wa Junansu Al-kur’ani A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Siyasa

Masu iya magana sun ce: siyasa ba da gaba ba, wanda ana iya cewa hakan ya saba lamba a Yobe ta Arewa, yayin da adawar siyasa ta dauki sabon salo tsakanin magoya bayan manyan yan siyasar yankin, al’amarin da ya kai ga zagayawa juna Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wani da daya bangaren adawar ke zargin namiji ne ya bude a Facebook wanda suke zargin yana cin zarafin mai gidansu a siyasa.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu a jihar cewa, akwai bangarori uku, wadanda basu ga-maciji da juna, wanda sun dade suna kai ruwa rana tare da jifar juna da miyagun kalamai, sannan kuma dukan su ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar ne.

  • Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas
  • Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

Bugu da kari kuma, majiyar ta kara da cewa, an samu wannan baraka ne tun bayan fitowar da hadimin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya yayi na takarar kujerar Majalisar Wakilai a Kananan Hukumomin Bade da Jakusko- Hon. Sani Ahmed Kaitafi, kana da bahallattsar da ta kaure tsakanin Sanata Lawan da Bashir Machina a takarar Sanatan Arewacin Yobe.

Adawar siyasa ta kara tsami ne a yan kwanakin nan sakamakon wani rubutun da wata mai ta’ammuli da turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’ ta yi wanda ya dada rura wutar adawar, wadda daya bangaren ya yi zargin cin zarafin Kwamishina a Ma’aikatar Kasafin Kudi a jihar Yobe, Hon. Muhammad Gagiyo wanda ya kai ga daukar matakin sauke Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wanda ake zargin.

LEADERSHIP ta tuntubi Mallam Ibrahim Babagana, Shugaban kungiyar ‘Gagiyo Youths Banguard’ da ke Gashu’a, dangane da makasudin kewaya Al-Kur’anin wanda ya fara da bayyana cewa, “Ba kewaya Al-Kur’ani muka yi ba, face kawai mun gayyato manyan mallammai da ke cikin garin Gashu’a domin mu karanta Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya matsayin sadaka da nufin Allah ya tona asirin wanda ya kirkiri turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’. Saboda yadda mai wannan sunan ya fake yana cin zarafin manyanmu.”

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

“Mun dauki wannan matakin ne ta hanyar gudanar da addu’ar Allah ya tona asirin sa da duk wanda yake goya masa baya. Musamman abin da ya faru kwanan nan inda mai wancan turakar ya yi wa jagoranmu, Hon. Muhammad Gagiyo kazafin da ya saba da al’ada da addinin musulunci. Saboda a matsayin Hon. Kwamishina, mutum ne mai mutunci kuma yana da iyalai, yan uwa da surukai, ace irin wannan zai faru kuma ayi shuru, sam bai dace ba.” In ji shi.

Mallam Babagana ya ce, ba yanzu ne hakan ya sha faruwa ba, wajen amfani da kafofin sada zumunta a yi wa dattawa da manyan mutane masu daraja kazafi ko cin mutunci. Ya ce, “Abin ne yayi yawa, kuma mun ga ya dace mu dauki tsauraran matakan shawo kan wannan matsalar.” Ya nanata.

Tuni dai wannan matakin ya jawo cece-kuce tare da rabuwar kawuna, inda wasu ke kallon matakin yayi tsauri, tare da ishara da cewa haka siyasa ta gada, yayin da wasu ke ganin hakan ya dace saboda gani ga wane ya ishi wane wa’azi.

Har wala yau, wasu kuma kira suka yi ga bangarorin da cewa a kai zukata nesa tare da yin adawar siyasa mai tsabta, tare da kiran bai-daya ga shugabannin siyasar Arewacin Yobe, da ma jihar baki daya cewa su rinka kaffa-kaffa da kalaman da ya dace suna furtawa, kana su ja kunnen magoya bayansu da yi musu tilawar muhimmancin zaman lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
Manyan Labarai

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Next Post
Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.