• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

by Sadiq
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

Gwamnonin Jihohi uku da ke kan karagar mulki sun shiga komar EFCC kan yunkurin karkatar da kudade ta hanyar biyan albashin ma’aikatan jihohinsu.

Shugaban Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, Abdulrasheed Bawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

  • Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama
  • Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Bawa, wanda bai bayyana sunayen gwamnonin ba, ya ce biyu daga cikinsu ‘yan Arewa ne, yayin da na ukun ya fito ne daga kudancin kasar nan.

Ya ce bayanan da hukumar ta samu sun nuna cewa gwamnonin uku sun kammala shirye-shiryen shigar da kudaden a cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan jiharsu.

“Bari na fada muku wani abu; bayanin da nake da shi jiya kuma zan so ku dauki wannan abu da muhimmanci. Tuni dai wasu gwamnonin jihohin suna da wasu makudan kudaden da aka boye a gidaje daban-daban, sauran kuma suna kokarin biyan kudin cikin tsarin albashi a jiharsu,”

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

kamar yadda ya shaida wa Daily Trust.

Da aka yi masa tambayoyi kan ko hukumar za ta gayyaci gwamnonin, Bawa ya ce suna sa ido sosai a kan su.

“Ban san yadda suke son cimma hakan ba amma dole ne mu hana su yin hakan. Muna aiki, har yanzu ba su biya albashin da tsabar kudi ba amma abu ne mai matukar mamaki,” in ji shi, inda ya ce matakin ya sabawa sashe na 2 na dokar hana barnar kudade.

“Dokar ta fito karara game da hada-hadar kudi. Duk wanda zai ci gaba da duk wata mu’amalar kudi a matsayinsa na mutum, idan ba ta hanyar hada-hadar kudi ba, to bai kamata ya wuce miliyan 5 ba, kuma idan ya kai sama da haka ya zama laifi a gare ku.

“Eh, na yarda albashin bai kai haka ba amma me ya sa kwatsam suka koma biyan mutane albashi ta ta hannu a maimakon asusun ajiyarsu na banki?

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya ke yunkurin sake fasalin takardun kudi na N200, N500 da N1000.

A ranar 26 ga watan Oktoba ne CBN ya sanar da cewa za a sake fasalin kudin kasar nan don magance matsaloli da dama da ke da illa ga tattalin arzikin Nijeriya.

Tags: BawaCBNEFCCGwamnoniSauya Fasalin Naira
Previous Post

Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama

Next Post

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Related

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

1 day ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

1 day ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

1 day ago
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike
Manyan Labarai

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

2 days ago
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari
Manyan Labarai

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

2 days ago
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

2 days ago
Next Post
Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.