ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

by Sadiq
4 years ago
EFCC

Gwamnonin Jihohi uku da ke kan karagar mulki sun shiga komar EFCC kan yunkurin karkatar da kudade ta hanyar biyan albashin ma’aikatan jihohinsu.

Shugaban Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, Abdulrasheed Bawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

  • Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama
  • Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Bawa, wanda bai bayyana sunayen gwamnonin ba, ya ce biyu daga cikinsu ‘yan Arewa ne, yayin da na ukun ya fito ne daga kudancin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Ya ce bayanan da hukumar ta samu sun nuna cewa gwamnonin uku sun kammala shirye-shiryen shigar da kudaden a cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan jiharsu.

“Bari na fada muku wani abu; bayanin da nake da shi jiya kuma zan so ku dauki wannan abu da muhimmanci. Tuni dai wasu gwamnonin jihohin suna da wasu makudan kudaden da aka boye a gidaje daban-daban, sauran kuma suna kokarin biyan kudin cikin tsarin albashi a jiharsu,”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

kamar yadda ya shaida wa Daily Trust.

Da aka yi masa tambayoyi kan ko hukumar za ta gayyaci gwamnonin, Bawa ya ce suna sa ido sosai a kan su.

“Ban san yadda suke son cimma hakan ba amma dole ne mu hana su yin hakan. Muna aiki, har yanzu ba su biya albashin da tsabar kudi ba amma abu ne mai matukar mamaki,” in ji shi, inda ya ce matakin ya sabawa sashe na 2 na dokar hana barnar kudade.

“Dokar ta fito karara game da hada-hadar kudi. Duk wanda zai ci gaba da duk wata mu’amalar kudi a matsayinsa na mutum, idan ba ta hanyar hada-hadar kudi ba, to bai kamata ya wuce miliyan 5 ba, kuma idan ya kai sama da haka ya zama laifi a gare ku.

“Eh, na yarda albashin bai kai haka ba amma me ya sa kwatsam suka koma biyan mutane albashi ta ta hannu a maimakon asusun ajiyarsu na banki?

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya ke yunkurin sake fasalin takardun kudi na N200, N500 da N1000.

A ranar 26 ga watan Oktoba ne CBN ya sanar da cewa za a sake fasalin kudin kasar nan don magance matsaloli da dama da ke da illa ga tattalin arzikin Nijeriya.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.