ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adawar Siyasa: ‘Yan Siyasa Sun Fara Kewaya Wa Junansu Al-kur’ani A Yobe

by Muhammad Maitela
4 years ago
Siyasa

Masu iya magana sun ce: siyasa ba da gaba ba, wanda ana iya cewa hakan ya saba lamba a Yobe ta Arewa, yayin da adawar siyasa ta dauki sabon salo tsakanin magoya bayan manyan yan siyasar yankin, al’amarin da ya kai ga zagayawa juna Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wani da daya bangaren adawar ke zargin namiji ne ya bude a Facebook wanda suke zargin yana cin zarafin mai gidansu a siyasa.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu a jihar cewa, akwai bangarori uku, wadanda basu ga-maciji da juna, wanda sun dade suna kai ruwa rana tare da jifar juna da miyagun kalamai, sannan kuma dukan su ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar ne.

  • Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas
  • Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

Bugu da kari kuma, majiyar ta kara da cewa, an samu wannan baraka ne tun bayan fitowar da hadimin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya yayi na takarar kujerar Majalisar Wakilai a Kananan Hukumomin Bade da Jakusko- Hon. Sani Ahmed Kaitafi, kana da bahallattsar da ta kaure tsakanin Sanata Lawan da Bashir Machina a takarar Sanatan Arewacin Yobe.

ADVERTISEMENT

Adawar siyasa ta kara tsami ne a yan kwanakin nan sakamakon wani rubutun da wata mai ta’ammuli da turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’ ta yi wanda ya dada rura wutar adawar, wadda daya bangaren ya yi zargin cin zarafin Kwamishina a Ma’aikatar Kasafin Kudi a jihar Yobe, Hon. Muhammad Gagiyo wanda ya kai ga daukar matakin sauke Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wanda ake zargin.

LEADERSHIP ta tuntubi Mallam Ibrahim Babagana, Shugaban kungiyar ‘Gagiyo Youths Banguard’ da ke Gashu’a, dangane da makasudin kewaya Al-Kur’anin wanda ya fara da bayyana cewa, “Ba kewaya Al-Kur’ani muka yi ba, face kawai mun gayyato manyan mallammai da ke cikin garin Gashu’a domin mu karanta Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya matsayin sadaka da nufin Allah ya tona asirin wanda ya kirkiri turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’. Saboda yadda mai wannan sunan ya fake yana cin zarafin manyanmu.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Mun dauki wannan matakin ne ta hanyar gudanar da addu’ar Allah ya tona asirin sa da duk wanda yake goya masa baya. Musamman abin da ya faru kwanan nan inda mai wancan turakar ya yi wa jagoranmu, Hon. Muhammad Gagiyo kazafin da ya saba da al’ada da addinin musulunci. Saboda a matsayin Hon. Kwamishina, mutum ne mai mutunci kuma yana da iyalai, yan uwa da surukai, ace irin wannan zai faru kuma ayi shuru, sam bai dace ba.” In ji shi.

Mallam Babagana ya ce, ba yanzu ne hakan ya sha faruwa ba, wajen amfani da kafofin sada zumunta a yi wa dattawa da manyan mutane masu daraja kazafi ko cin mutunci. Ya ce, “Abin ne yayi yawa, kuma mun ga ya dace mu dauki tsauraran matakan shawo kan wannan matsalar.” Ya nanata.

Tuni dai wannan matakin ya jawo cece-kuce tare da rabuwar kawuna, inda wasu ke kallon matakin yayi tsauri, tare da ishara da cewa haka siyasa ta gada, yayin da wasu ke ganin hakan ya dace saboda gani ga wane ya ishi wane wa’azi.

Har wala yau, wasu kuma kira suka yi ga bangarorin da cewa a kai zukata nesa tare da yin adawar siyasa mai tsabta, tare da kiran bai-daya ga shugabannin siyasar Arewacin Yobe, da ma jihar baki daya cewa su rinka kaffa-kaffa da kalaman da ya dace suna furtawa, kana su ja kunnen magoya bayansu da yi musu tilawar muhimmancin zaman lafiya.

Siyasa
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.