• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adawar Siyasa: ‘Yan Siyasa Sun Fara Kewaya Wa Junansu Al-kur’ani A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Adawar Siyasa: ‘Yan Siyasa Sun Fara Kewaya Wa Junansu Al-kur’ani A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu iya magana sun ce: siyasa ba da gaba ba, wanda ana iya cewa hakan ya saba lamba a Yobe ta Arewa, yayin da adawar siyasa ta dauki sabon salo tsakanin magoya bayan manyan yan siyasar yankin, al’amarin da ya kai ga zagayawa juna Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wani da daya bangaren adawar ke zargin namiji ne ya bude a Facebook wanda suke zargin yana cin zarafin mai gidansu a siyasa.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu a jihar cewa, akwai bangarori uku, wadanda basu ga-maciji da juna, wanda sun dade suna kai ruwa rana tare da jifar juna da miyagun kalamai, sannan kuma dukan su ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar ne.

  • Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas
  • Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

Bugu da kari kuma, majiyar ta kara da cewa, an samu wannan baraka ne tun bayan fitowar da hadimin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya yayi na takarar kujerar Majalisar Wakilai a Kananan Hukumomin Bade da Jakusko- Hon. Sani Ahmed Kaitafi, kana da bahallattsar da ta kaure tsakanin Sanata Lawan da Bashir Machina a takarar Sanatan Arewacin Yobe.

Adawar siyasa ta kara tsami ne a yan kwanakin nan sakamakon wani rubutun da wata mai ta’ammuli da turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’ ta yi wanda ya dada rura wutar adawar, wadda daya bangaren ya yi zargin cin zarafin Kwamishina a Ma’aikatar Kasafin Kudi a jihar Yobe, Hon. Muhammad Gagiyo wanda ya kai ga daukar matakin sauke Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya domin tona asirin wanda ake zargin.

LEADERSHIP ta tuntubi Mallam Ibrahim Babagana, Shugaban kungiyar ‘Gagiyo Youths Banguard’ da ke Gashu’a, dangane da makasudin kewaya Al-Kur’anin wanda ya fara da bayyana cewa, “Ba kewaya Al-Kur’ani muka yi ba, face kawai mun gayyato manyan mallammai da ke cikin garin Gashu’a domin mu karanta Al-Kur’ani Mai Girma tare da yanka saniya matsayin sadaka da nufin Allah ya tona asirin wanda ya kirkiri turakar Facebook mai suna ‘Maryam Yusuf Dachiya’. Saboda yadda mai wannan sunan ya fake yana cin zarafin manyanmu.”

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

“Mun dauki wannan matakin ne ta hanyar gudanar da addu’ar Allah ya tona asirin sa da duk wanda yake goya masa baya. Musamman abin da ya faru kwanan nan inda mai wancan turakar ya yi wa jagoranmu, Hon. Muhammad Gagiyo kazafin da ya saba da al’ada da addinin musulunci. Saboda a matsayin Hon. Kwamishina, mutum ne mai mutunci kuma yana da iyalai, yan uwa da surukai, ace irin wannan zai faru kuma ayi shuru, sam bai dace ba.” In ji shi.

Mallam Babagana ya ce, ba yanzu ne hakan ya sha faruwa ba, wajen amfani da kafofin sada zumunta a yi wa dattawa da manyan mutane masu daraja kazafi ko cin mutunci. Ya ce, “Abin ne yayi yawa, kuma mun ga ya dace mu dauki tsauraran matakan shawo kan wannan matsalar.” Ya nanata.

Tuni dai wannan matakin ya jawo cece-kuce tare da rabuwar kawuna, inda wasu ke kallon matakin yayi tsauri, tare da ishara da cewa haka siyasa ta gada, yayin da wasu ke ganin hakan ya dace saboda gani ga wane ya ishi wane wa’azi.

Har wala yau, wasu kuma kira suka yi ga bangarorin da cewa a kai zukata nesa tare da yin adawar siyasa mai tsabta, tare da kiran bai-daya ga shugabannin siyasar Arewacin Yobe, da ma jihar baki daya cewa su rinka kaffa-kaffa da kalaman da ya dace suna furtawa, kana su ja kunnen magoya bayansu da yi musu tilawar muhimmancin zaman lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdawaKalamaiKamfeMusayaSiyasaYankaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kone Maboyar Masu Garkuwa A Jigawa

Next Post

Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Next Post
Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

Matakan Da Suka Kamata A Bi Wajen Hada Abincin Kaji Don Su Yi Saurin Girma

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.