• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Gabanin Wasan Karshe

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Manyan Labarai, Rahotonni, Wasanni
0
AFCON 2023: Kasar Da Ta Lashe Kofi Zata Samu Dala Miliyan 7, Ta Biyu Kuma Dala Miliyan 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kowace shekara gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON tana kayatarwa ta hanyar kafa tarihi da kuma abubuwan mamaki da ake yi a gasar. Sai dai gasar da aka yi wadda aka buga a kasar Kamaru wadda kasar Senegal ta lashe ita ce gasar da aka buga da aka samu karancin zura kwallaye a raga, inda aka zura kwallo 100 cif.

Amma a wannan gasar wadda ake bugawa a kasar Ivory Coast, gasar ta zama ta daban duba da irin abubuwan da suka faru.

  • AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi
  • Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

Gasar AFCON 2023 da ake yi yanzu ita ce gasar da aka fi zura kwallo a raga cikin shekaru 13 da suka gabata.

Daya daga cikin dalilan da yasa aka zura kwallaye a raga a wannan lokacin shi ne; yanayin yadda kwallon kafa ya canja a duniya, kowa yana kokari wajen kai hari domin samun nasara. Kasashe da yawa da suka halarci gasar ta bana sun mayar da hankali ne wajen neman hanyar zura kwallo a raga ta hanyar samar da hanyoyin cin kwallaye.

Bugu da kari, kwarewar yan wasan gaba daga kasashen daban-daban ya samar da hanyoyin zura kwallo a raga saboda an samu kwararrun yan wasan gaba a wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Sannan yadda masu horar da kasashen suma suka dukufa wajen nemo hanyoyin zura kwallo a raga ya taimaka kasancewar an samu canje-canje a duniya musamman wajen shirya yadda za a ci kwallo.

MANYAN ‘YAN WASA SUN KASA KOMAI

Manyan ‘yan wasa da ake ganin tauraruwarsu za ta haska sun kasa tabuka abin azo a gani, wanda hakan yasa da yawa daga cikin manyan kasashen su suka kasa yin nisa a gasar saboda gazawar manyan ‘yan wasan wajen fitar da su kunya.

Manyan ‘yan wasan da suka gaza tabuka abin azo a gani a kasashen su sun hada da Mohamed Salah da Riyad Mahrez da Achraf Hakimi da Mohamed Kudus da dai sauran su.

Kazalika, dan wasa, Victor Osimhen na Nigeria, shi ne kusan jagoran tawagar ‘yan wasan duk da cewa ba shi ne kaftin ba, amma kusan shi ne wanda yake karfafa guiwar ‘yan wasa a cikin fili, sannan kasancewarsa gwarzon dan wasan Afirka yasa ana ganin ya zama kashin bayan tawagar.

Sai dai duk da haka, kwallo daya kacal ya iya zura wa a raga tun wasan farko sai, dai zai yi fatan ganin ya zura kwallo a wasan karshe.

Sakamakon gazawar manyan ‘yan wasa da kasashen su a gasar ta bana, an samu kasashe da ‘yan wasan su kuma tauraruwarsu ta haska, kamar tawagar ‘yan wasan kasar Cape Verde, musamman dan wasan su na baya Logan Costa, mai shekara 22 a duniya.

Sai dan wasan gaba na Equatorial Guinea, Emilio Nsue, wanda ya zura kwallo uku rigis a wasa daya a cikin rukuni, kuma rabon da a samu dan wasa ya zura kwallo uku a wasa daya tun shekara ta 2008. Sannan har ila yau, shi ne dan wasan da yafi zura kwallo a gasar bana, inda yake da kwallaye biyar.

Sai wanda ya nuna wata bajintar, mai tsaron ragar Afirka ta Kudu, kuma kaftin ɗin tawagar, Ronwen Williams, wanda ya kafa tarihin mai tsaron ragar da ya buge bugun daga kai sai mai tsaron raga guda hudu a wasa daya. A wasan da suka doke kasar Cape Verde.

Wasan karshe da za a buga a gobe Lahadi 11/02/20224, zai kasance mai zafi domin mai masaukin baki za ta yi fatan lashe kofin yayin da Nigeria ma za ta yi kokarin ganin ta dawo gida da kofin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AFCONAFCON 2023HasasheNigeria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Ke Gaban Real Madrid A Wannan Watan

Next Post

Kasashen Saudiyya Da Birtaniya Za Su Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Bangaren Hakar Ma’adanai

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

18 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

21 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

23 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

23 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

1 day ago
Next Post
saudiyya

Kasashen Saudiyya Da Birtaniya Za Su Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Bangaren Hakar Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.