• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Gabanin Wasan Karshe

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni, Wasanni
0
AFCON 2023: Kasar Da Ta Lashe Kofi Zata Samu Dala Miliyan 7, Ta Biyu Kuma Dala Miliyan 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kowace shekara gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON tana kayatarwa ta hanyar kafa tarihi da kuma abubuwan mamaki da ake yi a gasar. Sai dai gasar da aka yi wadda aka buga a kasar Kamaru wadda kasar Senegal ta lashe ita ce gasar da aka buga da aka samu karancin zura kwallaye a raga, inda aka zura kwallo 100 cif.

Amma a wannan gasar wadda ake bugawa a kasar Ivory Coast, gasar ta zama ta daban duba da irin abubuwan da suka faru.

  • AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi
  • Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

Gasar AFCON 2023 da ake yi yanzu ita ce gasar da aka fi zura kwallo a raga cikin shekaru 13 da suka gabata.

Daya daga cikin dalilan da yasa aka zura kwallaye a raga a wannan lokacin shi ne; yanayin yadda kwallon kafa ya canja a duniya, kowa yana kokari wajen kai hari domin samun nasara. Kasashe da yawa da suka halarci gasar ta bana sun mayar da hankali ne wajen neman hanyar zura kwallo a raga ta hanyar samar da hanyoyin cin kwallaye.

Bugu da kari, kwarewar yan wasan gaba daga kasashen daban-daban ya samar da hanyoyin zura kwallo a raga saboda an samu kwararrun yan wasan gaba a wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Sannan yadda masu horar da kasashen suma suka dukufa wajen nemo hanyoyin zura kwallo a raga ya taimaka kasancewar an samu canje-canje a duniya musamman wajen shirya yadda za a ci kwallo.

MANYAN ‘YAN WASA SUN KASA KOMAI

Manyan ‘yan wasa da ake ganin tauraruwarsu za ta haska sun kasa tabuka abin azo a gani, wanda hakan yasa da yawa daga cikin manyan kasashen su suka kasa yin nisa a gasar saboda gazawar manyan ‘yan wasan wajen fitar da su kunya.

Manyan ‘yan wasan da suka gaza tabuka abin azo a gani a kasashen su sun hada da Mohamed Salah da Riyad Mahrez da Achraf Hakimi da Mohamed Kudus da dai sauran su.

Kazalika, dan wasa, Victor Osimhen na Nigeria, shi ne kusan jagoran tawagar ‘yan wasan duk da cewa ba shi ne kaftin ba, amma kusan shi ne wanda yake karfafa guiwar ‘yan wasa a cikin fili, sannan kasancewarsa gwarzon dan wasan Afirka yasa ana ganin ya zama kashin bayan tawagar.

Sai dai duk da haka, kwallo daya kacal ya iya zura wa a raga tun wasan farko sai, dai zai yi fatan ganin ya zura kwallo a wasan karshe.

Sakamakon gazawar manyan ‘yan wasa da kasashen su a gasar ta bana, an samu kasashe da ‘yan wasan su kuma tauraruwarsu ta haska, kamar tawagar ‘yan wasan kasar Cape Verde, musamman dan wasan su na baya Logan Costa, mai shekara 22 a duniya.

Sai dan wasan gaba na Equatorial Guinea, Emilio Nsue, wanda ya zura kwallo uku rigis a wasa daya a cikin rukuni, kuma rabon da a samu dan wasa ya zura kwallo uku a wasa daya tun shekara ta 2008. Sannan har ila yau, shi ne dan wasan da yafi zura kwallo a gasar bana, inda yake da kwallaye biyar.

Sai wanda ya nuna wata bajintar, mai tsaron ragar Afirka ta Kudu, kuma kaftin ɗin tawagar, Ronwen Williams, wanda ya kafa tarihin mai tsaron ragar da ya buge bugun daga kai sai mai tsaron raga guda hudu a wasa daya. A wasan da suka doke kasar Cape Verde.

Wasan karshe da za a buga a gobe Lahadi 11/02/20224, zai kasance mai zafi domin mai masaukin baki za ta yi fatan lashe kofin yayin da Nigeria ma za ta yi kokarin ganin ta dawo gida da kofin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AFCONAFCON 2023HasasheNigeria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Ke Gaban Real Madrid A Wannan Watan

Next Post

Kasashen Saudiyya Da Birtaniya Za Su Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Bangaren Hakar Ma’adanai

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

5 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

13 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

13 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

14 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

17 hours ago
Next Post
saudiyya

Kasashen Saudiyya Da Birtaniya Za Su Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Bangaren Hakar Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.