• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: Abubuwan Da Suka Faru Gabanin Wasan Karshe

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
AFCON

A kowace shekara gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON tana kayatarwa ta hanyar kafa tarihi da kuma abubuwan mamaki da ake yi a gasar. Sai dai gasar da aka yi wadda aka buga a kasar Kamaru wadda kasar Senegal ta lashe ita ce gasar da aka buga da aka samu karancin zura kwallaye a raga, inda aka zura kwallo 100 cif.

Amma a wannan gasar wadda ake bugawa a kasar Ivory Coast, gasar ta zama ta daban duba da irin abubuwan da suka faru.

  • AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi
  • Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON

Gasar AFCON 2023 da ake yi yanzu ita ce gasar da aka fi zura kwallo a raga cikin shekaru 13 da suka gabata.

Daya daga cikin dalilan da yasa aka zura kwallaye a raga a wannan lokacin shi ne; yanayin yadda kwallon kafa ya canja a duniya, kowa yana kokari wajen kai hari domin samun nasara. Kasashe da yawa da suka halarci gasar ta bana sun mayar da hankali ne wajen neman hanyar zura kwallo a raga ta hanyar samar da hanyoyin cin kwallaye.

Bugu da kari, kwarewar yan wasan gaba daga kasashen daban-daban ya samar da hanyoyin zura kwallo a raga saboda an samu kwararrun yan wasan gaba a wannan shekarar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Sannan yadda masu horar da kasashen suma suka dukufa wajen nemo hanyoyin zura kwallo a raga ya taimaka kasancewar an samu canje-canje a duniya musamman wajen shirya yadda za a ci kwallo.

MANYAN ‘YAN WASA SUN KASA KOMAI

Manyan ‘yan wasa da ake ganin tauraruwarsu za ta haska sun kasa tabuka abin azo a gani, wanda hakan yasa da yawa daga cikin manyan kasashen su suka kasa yin nisa a gasar saboda gazawar manyan ‘yan wasan wajen fitar da su kunya.

Manyan ‘yan wasan da suka gaza tabuka abin azo a gani a kasashen su sun hada da Mohamed Salah da Riyad Mahrez da Achraf Hakimi da Mohamed Kudus da dai sauran su.

Kazalika, dan wasa, Victor Osimhen na Nigeria, shi ne kusan jagoran tawagar ‘yan wasan duk da cewa ba shi ne kaftin ba, amma kusan shi ne wanda yake karfafa guiwar ‘yan wasa a cikin fili, sannan kasancewarsa gwarzon dan wasan Afirka yasa ana ganin ya zama kashin bayan tawagar.

Sai dai duk da haka, kwallo daya kacal ya iya zura wa a raga tun wasan farko sai, dai zai yi fatan ganin ya zura kwallo a wasan karshe.

Sakamakon gazawar manyan ‘yan wasa da kasashen su a gasar ta bana, an samu kasashe da ‘yan wasan su kuma tauraruwarsu ta haska, kamar tawagar ‘yan wasan kasar Cape Verde, musamman dan wasan su na baya Logan Costa, mai shekara 22 a duniya.

Sai dan wasan gaba na Equatorial Guinea, Emilio Nsue, wanda ya zura kwallo uku rigis a wasa daya a cikin rukuni, kuma rabon da a samu dan wasa ya zura kwallo uku a wasa daya tun shekara ta 2008. Sannan har ila yau, shi ne dan wasan da yafi zura kwallo a gasar bana, inda yake da kwallaye biyar.

Sai wanda ya nuna wata bajintar, mai tsaron ragar Afirka ta Kudu, kuma kaftin ɗin tawagar, Ronwen Williams, wanda ya kafa tarihin mai tsaron ragar da ya buge bugun daga kai sai mai tsaron raga guda hudu a wasa daya. A wasan da suka doke kasar Cape Verde.

Wasan karshe da za a buga a gobe Lahadi 11/02/20224, zai kasance mai zafi domin mai masaukin baki za ta yi fatan lashe kofin yayin da Nigeria ma za ta yi kokarin ganin ta dawo gida da kofin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Next Post
saudiyya

Kasashen Saudiyya Da Birtaniya Za Su Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Bangaren Hakar Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.